• Gida
  • Game da Mu
  • Tuntuɓar
  • Advertise
  • Privacy & Policy
Kasuwancin Duniya
Advertisement
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
No Result
View All Result
Kasuwancin Duniya
No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
  • Al’adu da Fasaha
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
Home Labarai

NNPC Ltd Ta Sake Jaddada Kudurinta na Zaman Lafiya da Ci Gaban Makamashi Mai Dorewa a Ogoniland

December 24, 2025
in Labarai
Reading Time: 3 mins read
0
NNPC Ltd Ta Sake Jaddada Kudurinta na Zaman Lafiya da Ci Gaban Makamashi Mai Dorewa a Ogoniland

Daga dama zuwa hagu: Shugaban Kamfanin NNPC Ltd, Injiniya Bashir Bayo Ojulari (na biyu daga dama) tare da Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro, Mallam Nuhu Ribadu; Gwamnan Jihar Rivers, Sir Siminalayi Fubara; Ministan Ayyuka, Dave Umahi da Ministan Muhalli, Mallam Balarabe Lawal, yayin ziyarar tawagar Gwamnatin Tarayya zuwa Ogoniland, a Jihar Rivers, ranar Litinin.

0
SHARES
5
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsApp

Daga dama zuwa hagu: Shugaban Kamfanin NNPC Ltd, Injiniya Bashir Bayo Ojulari (na biyu daga dama) tare da Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro, Mallam Nuhu Ribadu; Gwamnan Jihar Rivers, Sir Siminalayi Fubara; Ministan Ayyuka, Dave Umahi da Ministan Muhalli, Mallam Balarabe Lawal, yayin ziyarar tawagar Gwamnatin Tarayya zuwa Ogoniland, a Jihar Rivers, ranar Litinin.
Shugaban NNPC Ltd, Injiniya Bashir Bayo Ojulari yana tattaunawa da ɗan asalin Ogoni yayin ziyarar tawagar Gwamnatin Tarayya zuwa Ogoniland, a Jihar Rivers, ranar Litinin.

Daga Bashir Bello

Karanta HakananPosts

Hon. Samaila Aliyu Makarfi Ya Taya Sanata Aminu Waziri Tambuwal Murnar Cikar Shekaru 60 da Haihuwa

Dangote Ya Janye Korafi Akan Tsohon Shugaban NMDPRA, Amma ICPC Ta Ce Bincike Zai Ci Gaba

Dangote Cement Na Taimakawa Al’ummomin Benue Ta Hanyar Ayyuka Masu Ma’ana inji Gwamnatin Tarayya

A wani mataki mai muhimmanci na sulhu da ci gaban da zai dore, Kamfanin Man Fetur na Ƙasa (NNPC Ltd.) ya sake jaddada aniyarsa na tabbatar da zaman lafiya, tattaunawa, da gudanar da ayyukan makamashi cikin gaskiya a yankin Ogoniland.

Wannan jaddadawa ta fito ne yayin wata ziyarar manyan jami’an Gwamnatin Tarayya zuwa yankin mai arzikin man fetur na Jihar Rivers a ranar Litinin.

A cewar wata sanarwa da Babban Jami’in Hulɗa da Jama’a na NNPC Ltd., Andy Odeh, ya sanya wa hannu, Shugaban Kamfanin NNPC Ltd., Injiniya Bashir Bayo Ojulari, ya bayyana wannan ziyara a matsayin “alamar cigaba” da kuma “sabon salo” ga al’ummar Ogoni. Ya jaddada cewa ƙoƙarin da Gwamnatin Tarayya ke yi a ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na nuni da sabon salo na haɗin gwiwa, girmama juna, da ɗaukar nauyin juna.

“Wannan ziyara na tabbatar da kudurin Gwamnatin Tarayya na zaman lafiya, tattaunawa, da dawo da amincewa,” in ji Ojulari. “A gare mu a NNPC Ltd., wannan sabon farawa ne da aka gina bisa haɗin kai, girmamawa da fahimtar juna.”

Ojulari ya bayyana tarihin wahala da yankin Ogoni ya fuskanta, yana mai cewa dole ne a fuskanci tarihi domin gina kyakkyawar makoma. Ya yaba da kwazon Kwamitin Shugaban Ƙasa kan Komawar Ogoni ƙarƙashin jagorancin Farfesa Don Baridam da kuma Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro, Mallam Nuhu Ribadu, bisa jagoranci da ƙoƙarinsu na gina amincewa da haɗin kai.

Yayin da yake bayyana manufar NNPC Ltd. a yankin, Ojulari ya ce burin kamfanin ya wuce kawai hako mai. “Muna da yakinin cewa ci gaban makamashi dole ne ya kasance tare da kare muhalli da walwalar al’umma,” in ji shi.

A wani muhimmin ci gaba, Ojulari ya sanar da cewa matasa 30 yan asalin Ogoni sun samu tayin aikin dindindin daga NNPC Ltd., kuma za su fara aiki a watan Janairu na shekarar 2026.

“Wannan mataki ne mai ma’ana wajen samun Damar ci gaban al’umma,” ya ƙara da cewa.

Gwamnan Jihar Rivers, Sir Siminalayi Fubara, wanda ya halarci taron, ya nuna godiya ga Shugaba Tinubu bisa jajircewarsa wajen warware matsalolin da suka dade suna damun yankin Ogoni. Ya bayyana cewa alkawuran da gwamnatin ta yi daga gine ginen ababen more rayuwa zuwa ilimi da samar da ayyukan yi, an Fara aiwatar Dasu.

“An tabbatar mana da ƙoƙarin gina amincewa, kafa Jami’ar Muhalli, asibitoci, filin masana’antu, da damar ayyukan yi,” in ji Fubara. “A yau, matasa maza da mata 30 ‘yan asalin Ogoni sun riga sun samu aikin NNPC Ltd.”

A madadin Shugaba Tinubu, Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro, Nuhu Ribadu, ya yaba wa al’ummar Ogoni da Gwamnatin Jihar Rivers bisa haɗin kai da goyon bayansu. “Muna nan yau saboda mutanen Ogoni, domin mu nuna godiya a madadin Najeriya,” in ji Ribadu. “Jihar Rivers yanzu na daga cikin jihohin da suka fi zaman lafiya a ƙasar nan, kuma hakan ya samu ne saboda jagorancin gwamna nagari da kuma kyawawan halayen al’ummar Ogoni.”

Ogoniland, inda ke ɗauke da filin hako mai na OML-11, na ci gaba da kasancewa muhimmin ginshiƙi a fannin makamashi na Najeriya. Kamfanin NNPC Exploration and Production Limited (NEPL), reshen NNPC Ltd., ne ke gudanar da ayyukan a OML-11, wanda shi ne mafi girma a cikin filayen hako mai na ƙasa, inda Ogoniland ke da fiye da kashi 40 cikin 100 na adadin man da za a iya fitarwa.

Yayin da Gwamnatin Tarayya da NNPC Ltd. ke ci gaba da tattaunawa da al’ummomin yankin, wannan ziyara ta ranar Litinin na nuna sabon babi, warkarwa, ci gaba, da walwala ga kowa a yankin Ogoniland.

Previous Post

Kamfanin Dangote Cement ta Kaddamar da Shirye shiryen Tallafin Al’umma da Darajarsu Ta Kai Miliyoyin Naira a Al’ummomin Gboko

Next Post

Saƙon Gaisuwa daga Kasuwanduniya.com

Related Posts

Hon. Samaila Aliyu Makarfi Ya Taya Sanata Aminu Waziri Tambuwal Murnar Cikar Shekaru 60 da Haihuwa
Labarai

Hon. Samaila Aliyu Makarfi Ya Taya Sanata Aminu Waziri Tambuwal Murnar Cikar Shekaru 60 da Haihuwa

January 11, 2026
Dangote Ya Janye Korafi Akan Tsohon Shugaban NMDPRA, Amma ICPC Ta Ce Bincike Zai Ci Gaba
Labarai

Dangote Ya Janye Korafi Akan Tsohon Shugaban NMDPRA, Amma ICPC Ta Ce Bincike Zai Ci Gaba

January 8, 2026
Labarai

Dangote Cement Na Taimakawa Al’ummomin Benue Ta Hanyar Ayyuka Masu Ma’ana inji Gwamnatin Tarayya

January 7, 2026
2026 Hajji: Shugaban NAHCON ya tafi Saudiyya domin kammala shirye-shirye
Labarai

2026 Hajji: Shugaban NAHCON ya tafi Saudiyya domin kammala shirye-shirye

January 4, 2026
Sakon Sabuwar Shekara
Labarai

Sakon Sabuwar Shekara

January 2, 2026
Gwamna Namadi Ya Amince da Nadin Jami’ai 27 Don Taimakawa Aikin Hajjin 2026 a Jigawa
Labarai

Gwamna Namadi Ya Amince da Nadin Jami’ai 27 Don Taimakawa Aikin Hajjin 2026 a Jigawa

December 31, 2025
Next Post
Saƙon Gaisuwa daga  Kasuwanduniya.com

Saƙon Gaisuwa daga Kasuwanduniya.com

KARFAFA HULDA DON TSARON KASA: SHUGABAN NESO YA KAI ZIYARAR GIRMAMAWA GA MINISTAN TSARO

KARFAFA HULDA DON TSARON KASA: SHUGABAN NESO YA KAI ZIYARAR GIRMAMAWA GA MINISTAN TSARO

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Trending
  • Comments
  • Latest
“Siyan wayoyin hannu na zuwa da babbar matsala” — Abubakar Ubale

“Siyan wayoyin hannu na zuwa da babbar matsala” — Abubakar Ubale

January 1, 2026
ADC ta samu babban jigo na siyasa Farfesa Sani Bello don aikin duba kundin tsarin mulki bayan Awanni 24 da barin APC

ADC Ta Nuna Sabuwar Zamanin Gaskiya da Aminci ta Hanyar Nada Farfesa Mohammed Sani Bell

January 8, 2026
Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta bukaci kungiyoyin likitocin jihohi da su bi ka’idojin kiwon lafiya na aikin Hajjin 2026 da Saudiyya ta fitar da tsattsauran ra’ayi.

Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta bukaci kungiyoyin likitocin jihohi da su bi ka’idojin kiwon lafiya na aikin Hajjin 2026 da Saudiyya ta fitar da tsattsauran ra’ayi.

December 30, 2025
Gwamnan Osun, Masana Ilimi da Sarakunan Gargajiya Za Su Halarci Bikin Cika Shekaru 40 na KIDVARC

Gwamnan Osun, Masana Ilimi da Sarakunan Gargajiya Za Su Halarci Bikin Cika Shekaru 40 na KIDVARC

November 26, 2025
Sanata Anthony Yaro Ya Gamsu Da Dokar Cin Zarafin yara

Sanata Anthony Yaro Ya Gamsu Da Dokar Cin Zarafin yara

0
Zamu Fara Bincike A Kan Matuka Jiragen Sama Don Hanasu Shan Kayan Maye, Inji Sanata Buhari Abdulfatah

Zamu Fara Bincike A Kan Matuka Jiragen Sama Don Hanasu Shan Kayan Maye, Inji Sanata Buhari Abdulfatah

0
Kudirin Dokar Cibiyar Hukumar EFCC Ta Tsallake karatu Na Biyu

Kudirin Dokar Cibiyar Hukumar EFCC Ta Tsallake karatu Na Biyu

0
Yan Majalisa da Ma’aikatar Yan Sanda sun goyi bayan kashi 15% na Mata Wurin daukar aiki

Yan Majalisa da Ma’aikatar Yan Sanda sun goyi bayan kashi 15% na Mata Wurin daukar aiki

0
Yadda ƴaƴan cashew ke rage ƙiba da haɗarin kamuwa da ciwon zuciya

Yadda ƴaƴan cashew ke rage ƙiba da haɗarin kamuwa da ciwon zuciya

January 15, 2026
Hon. Samaila Aliyu Makarfi Ya Taya Sanata Aminu Waziri Tambuwal Murnar Cikar Shekaru 60 da Haihuwa

Hon. Samaila Aliyu Makarfi Ya Taya Sanata Aminu Waziri Tambuwal Murnar Cikar Shekaru 60 da Haihuwa

January 11, 2026
ADC ta samu babban jigo na siyasa Farfesa Sani Bello don aikin duba kundin tsarin mulki bayan Awanni 24 da barin APC

ADC Ta Nuna Sabuwar Zamanin Gaskiya da Aminci ta Hanyar Nada Farfesa Mohammed Sani Bell

January 8, 2026
Dangote Ya Janye Korafi Akan Tsohon Shugaban NMDPRA, Amma ICPC Ta Ce Bincike Zai Ci Gaba

Dangote Ya Janye Korafi Akan Tsohon Shugaban NMDPRA, Amma ICPC Ta Ce Bincike Zai Ci Gaba

January 8, 2026

Recent News

Yadda ƴaƴan cashew ke rage ƙiba da haɗarin kamuwa da ciwon zuciya

Yadda ƴaƴan cashew ke rage ƙiba da haɗarin kamuwa da ciwon zuciya

January 15, 2026
Hon. Samaila Aliyu Makarfi Ya Taya Sanata Aminu Waziri Tambuwal Murnar Cikar Shekaru 60 da Haihuwa

Hon. Samaila Aliyu Makarfi Ya Taya Sanata Aminu Waziri Tambuwal Murnar Cikar Shekaru 60 da Haihuwa

January 11, 2026
ADC ta samu babban jigo na siyasa Farfesa Sani Bello don aikin duba kundin tsarin mulki bayan Awanni 24 da barin APC

ADC Ta Nuna Sabuwar Zamanin Gaskiya da Aminci ta Hanyar Nada Farfesa Mohammed Sani Bell

January 8, 2026
Dangote Ya Janye Korafi Akan Tsohon Shugaban NMDPRA, Amma ICPC Ta Ce Bincike Zai Ci Gaba

Dangote Ya Janye Korafi Akan Tsohon Shugaban NMDPRA, Amma ICPC Ta Ce Bincike Zai Ci Gaba

January 8, 2026
Kasuwancin Duniya

© 2025 Kasuwancin Duniya - Wanda ya tsara AuspiceWeb.

Kewaya Site

  • Gida
  • Game da Mu
  • Tuntuɓar
  • Advertise
  • Privacy & Policy

Biyo Mu

No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni

© 2025 Kasuwancin Duniya - Wanda ya tsara AuspiceWeb.

Powered by
...
►
Necessary cookies enable essential site features like secure log-ins and consent preference adjustments. They do not store personal data.
None
►
Functional cookies support features like content sharing on social media, collecting feedback, and enabling third-party tools.
None
►
Analytical cookies track visitor interactions, providing insights on metrics like visitor count, bounce rate, and traffic sources.
None
►
Advertisement cookies deliver personalized ads based on your previous visits and analyze the effectiveness of ad campaigns.
None
►
Unclassified cookies are cookies that we are in the process of classifying, together with the providers of individual cookies.
None
Powered by