• Gida
  • Game da Mu
  • Tuntuɓar
  • Advertise
  • Privacy & Policy
Kasuwancin Duniya
Advertisement
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
No Result
View All Result
Kasuwancin Duniya
No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
  • Al’adu da Fasaha
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
Home Kasuwanci

“Sayen Wayoyin Hannu Na Zuwa Da Mummunar Matsala” — Abubakar Ubale

Wannan fassarar hirar ce da aka yi da Abubakar Ubale, Shugaban Kamfanin MashaAllah Phone Accessories dake Bwari, Abuja.

January 18, 2026
in Kasuwanci
Reading Time: 3 mins read
0
“Sayen Wayoyin Hannu Na Zuwa Da Mummunar Matsala” — Abubakar Ubale

Abubakar Ubale shi ne Shugaban Kamfanin MashaAllah Phone Accessories.

0
SHARES
68
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsApp

Karanta HakananPosts

Kamfanin Siminti na Dangote Ta Fara Amfani da Fasahar AI da Telematics Don Ƙarfafa Tsaron Sufuri

Sabuwar Manufar Tsaron Hanyoyin Motar Dangote Na Haifar Da Kyakkyawan Sakamako In Ji Hukumar FRSC

Jihar Neja Na Neman Kamfanin Dangote Don Binciken Man Fetur a Yankin Bida

Abubakar Ubale shi ne Shugaban Kamfanin MashaAllah Phone Accessories dake kusa da Babban Masallacin Bwari. A wannan tattaunawa ta musamman da dan jarida Ahmed Aliyu, ya bayyana irin fadi-tashin da ya fuskanta a harkar sayar da wayoyi, inda ya tona asirin kalubalen dake cikin sana’ar da kuma hadarin dake tattare da sayen wayoyin hannu (second-hand).
Ga dai yadda hirar ta kasance:
Tambaya: Ni daga News Global Enterprise da Kauwanci Duniya nake, muna tallata kananan sana’o’i a fadin kasa. Za ka iya ba mu takaitaccen tarihin ka?
Abubakar Ubale: Sunana Abubakar Ubale, ni dan jihar Kano ne. An haife ni a Sharada Phase 1 a Kano. Na yi makarantar boko a can, sannan na tafi makarantar Allo a jihar Jigawa inda na shafe shekaru 10. Na dawo Kano, sannan na nufi Abuja neman na kaina. Na fara zama a Tafa, sannan na koma Maje, daga karshe na dawo Bwari.
Na fara sana’ar ne da cajin waya, sannan na koma sayar da wayoyin hannu (second-hand). Amma Allah ya kawo ranar da na daina cajin waya da sayar da wadannan wayoyin saboda hadarin dake ciki. Na fuskanci kalubale da yawa a lokacin. Ina godiya ga Allah da ya fitar da ni daga wannan matakin zuwa matsayin mai sayar da sabbin wayoyi da kuma wadanda aka kera a kasashen waje (London-used).
Tambaya: Yaushe ka fara wannan sana’ar, kuma shekarunka nawa a ciki?
Abubakar Ubale: Na kusa shafe shekaru 20 ina wannan harkar ta waya.
Tambaya: Menene ra’ayinka game da sana’ar waya?
Abubakar Ubale: A gaskiya ina godiya ga Allah. Sana’a ce mai riba sosai, amma tana da hadari da kalubale. Babban abin da mutum yake bukata shi ne hakuri, rashin kwadayi, da kuma tsantsar taka-tsantsan. Kana iya tunanin cewa sayen wayar hannu mai arha daga wajen abokin ciniki riba ce, amma gaskiyar magana ita ce wannan cinikin zai iya jefa ka cikin bakin ciki da masifa.
Tambaya: Shin kana nufin sayen wayoyin hannu (second-hand) na da hadari?
Abubakar Ubale: Kwarai kuwa, yana da matukar hadari. Sayen wayar hannu na zuwa da babbar matsala, shi ya sa na daina ma’amala da su. Misali, kana iya sayen waya, idan maganar ta kai ga ‘yan sanda ko jami’an tsaro, sai abin ya zama wani abu daban. Kuna iya sayen waya a kan naira dubu goma, amma idan aka kai ka caji-ofis, sai a ce wayar da aka yi fashi da ita ce. Za ka iya tsinci kanka kana kashe kudin da suka ninka dubu goma kafin ka kubuta. Don haka, ina ribar take? Wani lokacin ma tarkon ne ake dana wa mutum. Wani bako zai zo ya sayar maka da waya yau, washegari wani ya zo ya ce tasa ce, kafin ka ankara ka tsinci kanka a hannun ‘yan sanda. Wannan ya sa na koma sayar da wayoyin “London-used” kawai.
Su wayoyi ne da ake shigo da su kai tsaye daga kasar waje. Muna da samfura kamar Oppo, Vivo, Huawei, Redmi, ZTE da sauran su. Dillalai ne halastattu suke shigo da su Najeriya. Mu kuma muna zuwa kasuwanninmu mu zaba, mu biya kudi, mu kawo shagonmu mu tsara su, sannan mu sayar wa kwastomominmu tare da ba su takardar shaida (receipt). Tambaya: Mai ribar sanar waya?
Abubakar Ubale: Ina godiya ga Allah da na shiga wannan sana’a. Na fara ta ne tun ina gwauro, amma ta dalilin ta na yi aure; na auri matata ta farko da ta biyu duka a cikinta. Yanzu ina da mata biyu da ‘ya’ya shida. Sannan na gina gidaje guda biyu duka ta dalilin wannan sana’a. Ina godiya sosai.
Tambaya: Wadanne kalubale kake fuskanta a matsayinka na wanda ya yi shekara 20?
Abubakar Ubale: Daya daga cikin manyan matsalolinmu shi ne rashin hadin kai a kungiyarmu ta masu sayar da wayoyi a nan Bwari. Akwai rikicin shugabanci da rashin fahimtar juna. Wannan ya sa ko gwamnati na son taimaka mana, ba za mu iya samu ba saboda rashin hadin kai. Wasu mambobin dake sayar da wayoyin hannu (second-hand) suna jawo mana matsaloli saboda rashin bin shawarwari da dokoki. Saboda haka, na gwammace na ware kaina in yi sana’ata da tsoron Allah.
Tambaya: Wayoyi nawa kake sayarwa a rana daya?
Abubakar Ubale: Ya danganta da yanayin kasuwa. Wata ranar ana iya sayar da waya goma ko fiye, wata ranar kuma ba za a sayar ko daya ba. Amma yanzu waya ta zama kamar abinci ga kowa, don haka ba kasafai ake zama ba tare da an sayar da ko daya ba.
Tambaya: Wane shawara kake da shi ga masu son shiga wannan sana’a?
A

Abubakar Ubale Shugaban Kamfanin MashaAllah Phone Accessories.
bubakar Ubale: Shawarata ga masu sana’ar waya ita ce su kasance masu taka-tsantsan. Ba na cewa kada su sayar da wayoyin hannu (second-hand) ba, a’a, abin da nake nufi shi ne su kasance masu zargi da bincike. Su tabbatar sun sayi waya tare da takardar shaida (receipt) da kwalin wayar (carton) don guje wa matsala. Ga masu son shiga sana’ar kuma, su fara koyon aikin a karkashin kwararru, su kwantar da hankalinsu su koyi yadda ake yin harkar kafin su fara na kansu.

Previous Post

Gwamna Namadi Ya Amince da Nadin Jami’ai 27 Don Taimakawa Aikin Hajjin 2026 a Jigawa

Next Post

Sakon Sabuwar Shekara

Related Posts

Kamfanin Siminti na Dangote Ta Fara Amfani da Fasahar AI da Telematics Don Ƙarfafa Tsaron Sufuri
Kasuwanci

Kamfanin Siminti na Dangote Ta Fara Amfani da Fasahar AI da Telematics Don Ƙarfafa Tsaron Sufuri

June 7, 2026
Kasuwanci

Sabuwar Manufar Tsaron Hanyoyin Motar Dangote Na Haifar Da Kyakkyawan Sakamako In Ji Hukumar FRSC

May 26, 2026
Jihar Neja Na Neman Kamfanin Dangote Don Binciken Man Fetur a Yankin Bida
Kasuwanci

Jihar Neja Na Neman Kamfanin Dangote Don Binciken Man Fetur a Yankin Bida

May 24, 2026
Bikin Kasuwanci na Nasarawa: Dangote Ya Ce Aikin Yi Zai Ƙaru ‎
Kasuwanci

Bikin Kasuwanci na Nasarawa: Dangote Ya Ce Aikin Yi Zai Ƙaru ‎

May 3, 2026
Bikin Baje Kolin Kasuwanci: Gwamna Sule Ya Bukaci Kamfanin Dangote Ya Kara Zuba Jari a Nasarawa
Kasuwanci

Bikin Baje Kolin Kasuwanci: Gwamna Sule Ya Bukaci Kamfanin Dangote Ya Kara Zuba Jari a Nasarawa

April 26, 2026
Dangote Ya Haske Manufar Masana’antar Mai na 2030, Da Sauransu, A Bikin Kasuwanci Na Nasarawa
Kasuwanci

Dangote Ya Haske Manufar Masana’antar Mai na 2030, Da Sauransu, A Bikin Kasuwanci Na Nasarawa

April 16, 2026
Next Post
Sakon Sabuwar Shekara

Sakon Sabuwar Shekara

2026 Hajji: Shugaban NAHCON ya tafi Saudiyya domin kammala shirye-shirye

2026 Hajji: Shugaban NAHCON ya tafi Saudiyya domin kammala shirye-shirye

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Trending
  • Comments
  • Latest
“Sayen Wayoyin Hannu Na Zuwa Da Mummunar Matsala” — Abubakar Ubale

“Sayen Wayoyin Hannu Na Zuwa Da Mummunar Matsala” — Abubakar Ubale

January 18, 2026
TARON OPEN MIC WITH SHINE YAFARA YUNKURIN FARFAƊO DA ƊABI’U: MASU JAWABI SUN YABI HANGEN NESAN MR. SHINE

TARON OPEN MIC WITH SHINE YAFARA YUNKURIN FARFAƊO DA ƊABI’U: MASU JAWABI SUN YABI HANGEN NESAN MR. SHINE

June 20, 2026
BA Zamu Sake Yarda ayi Watsi da Matasa Bayan Zabe ba Inji Kungiyar NYA

BA Zamu Sake Yarda ayi Watsi da Matasa Bayan Zabe ba Inji Kungiyar NYA

January 28, 2026
ADC ta samu babban jigo na siyasa Farfesa Sani Bello don aikin duba kundin tsarin mulki bayan Awanni 24 da barin APC

ADC Ta Nuna Sabuwar Zamanin Gaskiya da Aminci ta Hanyar Nada Farfesa Mohammed Sani Bell

January 8, 2026
Sanata Anthony Yaro Ya Gamsu Da Dokar Cin Zarafin yara

Sanata Anthony Yaro Ya Gamsu Da Dokar Cin Zarafin yara

0
Zamu Fara Bincike A Kan Matuka Jiragen Sama Don Hanasu Shan Kayan Maye, Inji Sanata Buhari Abdulfatah

Zamu Fara Bincike A Kan Matuka Jiragen Sama Don Hanasu Shan Kayan Maye, Inji Sanata Buhari Abdulfatah

0
Kudirin Dokar Cibiyar Hukumar EFCC Ta Tsallake karatu Na Biyu

Kudirin Dokar Cibiyar Hukumar EFCC Ta Tsallake karatu Na Biyu

0
Yan Majalisa da Ma’aikatar Yan Sanda sun goyi bayan kashi 15% na Mata Wurin daukar aiki

Yan Majalisa da Ma’aikatar Yan Sanda sun goyi bayan kashi 15% na Mata Wurin daukar aiki

0
KAMFANIN DANGOTE CEMENT YA KADDAMAR DA KATAFAREN ASIBITI A JIHAR KOGI

KAMFANIN DANGOTE CEMENT YA KADDAMAR DA KATAFAREN ASIBITI A JIHAR KOGI

July 13, 2026
Gwamna Yusuf Ya Kai Ziyaran Gaisuwa da Girmamawa ga Mataimakin Shugaban Kasa Shettima, Ya Taya Shi Murna Bisa Fitowarsa a Matsayin Abokin Takaran Tinubu

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Garo a Matsayin Abokin Takararsa Domin Neman Zaben 2027

July 13, 2026
Gwamna Yusuf Ya Kai Ziyaran Gaisuwa da Girmamawa ga Mataimakin Shugaban Kasa Shettima, Ya Taya Shi Murna Bisa Fitowarsa a Matsayin Abokin Takaran Tinubu

Gwamna Yusuf Ya Kai Ziyaran Gaisuwa da Girmamawa ga Mataimakin Shugaban Kasa Shettima, Ya Taya Shi Murna Bisa Fitowarsa a Matsayin Abokin Takaran Tinubu

July 13, 2026
Gwamna Yusuf Ya Taya Shugaba Tinubu Murna Kan Mika Fom ɗin Neman Takarar INEC

Gwamna Yusuf Ya Taya Shugaba Tinubu Murna Kan Mika Fom ɗin Neman Takarar INEC

July 11, 2026

Recent News

KAMFANIN DANGOTE CEMENT YA KADDAMAR DA KATAFAREN ASIBITI A JIHAR KOGI

KAMFANIN DANGOTE CEMENT YA KADDAMAR DA KATAFAREN ASIBITI A JIHAR KOGI

July 13, 2026
Gwamna Yusuf Ya Kai Ziyaran Gaisuwa da Girmamawa ga Mataimakin Shugaban Kasa Shettima, Ya Taya Shi Murna Bisa Fitowarsa a Matsayin Abokin Takaran Tinubu

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Garo a Matsayin Abokin Takararsa Domin Neman Zaben 2027

July 13, 2026
Gwamna Yusuf Ya Kai Ziyaran Gaisuwa da Girmamawa ga Mataimakin Shugaban Kasa Shettima, Ya Taya Shi Murna Bisa Fitowarsa a Matsayin Abokin Takaran Tinubu

Gwamna Yusuf Ya Kai Ziyaran Gaisuwa da Girmamawa ga Mataimakin Shugaban Kasa Shettima, Ya Taya Shi Murna Bisa Fitowarsa a Matsayin Abokin Takaran Tinubu

July 13, 2026
Gwamna Yusuf Ya Taya Shugaba Tinubu Murna Kan Mika Fom ɗin Neman Takarar INEC

Gwamna Yusuf Ya Taya Shugaba Tinubu Murna Kan Mika Fom ɗin Neman Takarar INEC

July 11, 2026
Kasuwancin Duniya

© 2025 Kasuwancin Duniya - Wanda ya tsara AuspiceWeb.

Kewaya Site

  • Gida
  • Game da Mu
  • Tuntuɓar
  • Advertise
  • Privacy & Policy

Biyo Mu

No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni

© 2025 Kasuwancin Duniya - Wanda ya tsara AuspiceWeb.

Powered by
►
Necessary cookies enable essential site features like secure log-ins and consent preference adjustments. They do not store personal data.
None
►
Functional cookies support features like content sharing on social media, collecting feedback, and enabling third-party tools.
None
►
Analytical cookies track visitor interactions, providing insights on metrics like visitor count, bounce rate, and traffic sources.
None
►
Advertisement cookies deliver personalized ads based on your previous visits and analyze the effectiveness of ad campaigns.
None
►
Unclassified cookies are cookies that we are in the process of classifying, together with the providers of individual cookies.
None
Powered by