• Gida
  • Game da Mu
  • Tuntuɓar
  • Advertise
  • Privacy & Policy
Kasuwancin Duniya
Advertisement
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
No Result
View All Result
Kasuwancin Duniya
No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
  • Al’adu da Fasaha
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
Home Labarai

Dangote Ya Kaddamar da Tallafin Karatu na Naira Tiriliyan Daya

December 12, 2025
in Labarai
Reading Time: 3 mins read
0
Dangote Ya Kaddamar da Tallafin Karatu na Naira Tiriliyan Daya
0
SHARES
2
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsApp

Daga Bashir Bello

Alhaji Aliko Dangote, Shugaban Gidauniyar Aliko Dangote (ADF) kuma Shugaban Rukunin Kamfanonin Dangote, ya sanar da wani shirin tallafin karatu na Naira Tiriliyan Daya domin fadada damar samun ilimi da kuma karfafa hazaka a fadin Najeriya.

Karanta HakananPosts

Hon. Samaila Aliyu Makarfi Ya Taya Sanata Aminu Waziri Tambuwal Murnar Cikar Shekaru 60 da Haihuwa

Dangote Ya Janye Korafi Akan Tsohon Shugaban NMDPRA, Amma ICPC Ta Ce Bincike Zai Ci Gaba

Dangote Cement Na Taimakawa Al’ummomin Benue Ta Hanyar Ayyuka Masu Ma’ana inji Gwamnatin Tarayya

Wannan shiri zai fara aiki daga shekarar 2026, inda za a tallafa wa dalibai sama da miliyan 1.3 daga kananan hukumomi 774 na kasar, tare da ware Naira Biliyan 100 a kowace shekara na tsawon shekaru goma.

Shirin ya mayar da hankali ne kan daliban da suka fi bukata a Najeriya, kuma an raba shi zuwa rukuni uku:

Aliko Dangote STEM Scholars, Dalibai 30,000 a jami’o’in gwamnati da kwalejojin kimiyya za su samu tallafin karatun har zuwa Naira 600,000 a kowace shekara.

Aliko Dangote Technical Scholars, Matasa 5,000 masu koyon sana’o’in fasaha za su samu kayan karatu da na aikin hannu.

MHF Dangote Secondary School Girls Scholars, Yan mata 10,000 a makarantun sakandare na gwamnati za su samu kayan makaranta, littattafai da kayan koyarwa, musamman a jihohin da ke da yawan yara mata da ba sa zuwa makaranta.

Za a aiwatar da shirin ne tare da hadin gwiwar hukumomin NELFUND, JAMB, NIMC, NUC, NBTE, WAEC da NECO, ta hanyar tsarin tantancewa da rabon tallafi na zamani da ya dogara da cancanta.

Dangote ya bayyana cewa wannan wani muhimmin jari ne a bangaren ci gaban dan Adam, wanda zai rage gibin da ke tsakanin masu hali da marasa hali, tare da bunkasa ci gaban kasa.

An kafa kwamitin jagoranci na shirin karkashin jagorancin Mai Martaba Sarkin Lafia, Mai Shari’a Sidi Dauda Bage. Dangote ya sha alwashin ware kashi 25 cikin 100 na dukiyarsa domin dorewar shirin, wanda za a duba ci gaban sa a cikin tsarin hangen nesa na Dangote Group na shekarar 2030.

Dangote ya ce daliban da suka fi bukata ne za su fi amfana da wannan shiri, yana mai jaddada cewa rashin kudi ne ke hana yawancin matasa ci gaba da karatu, ba rashin basira ba. Ya ce wannan ba sadaka ba ce kawai, illa wani zuba jari ne mai zurfi a makomar Najeriya.

“Kowane yaro da muka taimaka ya ci gaba da karatu yana karfafa tattalin arzikinmu. Kowane dalibi da muka tallafa yana rage bambanci. Kowane mai karatu da muka karfafa zai zama ginshikin ci gaban kasa a nan gaba,” in ji shi.

Dangote ya kara da cewa Gidauniyar ADF ta dade tana mayar da hankali kan lafiya da abinci a matsayin ginshikan ci gaban dan Adam, amma halin tattalin arzikin yanzu ya sanya tallafin ilimi ya zama dole.

Ya ce: “Babu dalilin da zai sa matashi ya daina karatu saboda rashin kudi. Muna daukar mataki domin tabbatar da cewa dalibai sun ci gaba da karatu da cimma burinsu. Wannan shiri ya wuce tallafin kudi kawai, zuba jari ne a jikin dan Adam, wanda zai haifar da tasiri mai fadi a tattalin arziki, al’umma da kuma al’ummomi masu zuwa.”

Ya bayyana ilimi a matsayin “tushen kowace al’umma mai ci gaba,” yana mai cewa ilimi shi ne mafi karfi wajen daidaita bambance bambance da kuma bunkasa rayuwar jama’a. Duk da haka, ya gargadi cewa dalibai masu hazaka da dama a Najeriya na fuskantar matsin tattalin arziki da ke barazana ga ci gaban su. “Ba za mu yarda da talauci ya hana matasanmu cika burinsu ba musamman idan makomar kasar nan na dogara da basirar su, juriya da shugabancinsu,” in ji shi.

Shirin zai mayar da hankali kan sakamako mai auna tasiri kamar ci gaba da halartar makaranta, kammala karatu da tasirin bayan makaranta. Dangote ya ce burin wannan shiri shi ne bai wa kowane yaro mai cancanta damar karatu ba tare da shinge na kudi ba, tare da ‘yancin mafarki da kayan cimma nasara.

Mambobin kwamitin jagoranci sun hada da tsofaffin shugabannin jami’o’i, manyan jami’an ilimi, kwararru da wakilan dangin Dangote.

A jawabinsa, Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, ya yaba da hangen nesa da gudummawar Dangote ga ci gaban kasa, yana mai cewa wannan shiri ya nuna muhimmancin hadin gwiwar masu zaman kansu a ci gaban kasa.

Ya ce yawan jama’a a Najeriya na bukatar zuba jari cikin gaggawa a fannin ilimi, domin al’umma ba za ta ci gaba ba idan ba ta da ilimi.

Ministan Ilimi, Dr. Tunji Alausa, ya bayyana shirin a matsayin “cikakken ci gaban dan Adam,” yana mai cewa yana da daidaito da tsarin gwamnatin Tinubu na sauya Najeriya daga tattalin arzikin da ya dogara da albarkatu zuwa wanda ya dogara da ilimi.

Shima a jawabinsa, Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo Olu, ya wakilci sauran gwamnoni 36 wajen yabawa da kuma alkawarin goyon bayan su ga shirin.

Mai Martaba Sarkin Ife, Oba Adeyeye Enitan Ogunwusi, Ojaja II, ya bayyana wannan shiri a matsayin wani babban sauyi da kuma zuba jari mai ma’ana a makomar Najeriya, yana mai tuna yadda Gidauniyar ADF ta taimaka wa al’ummarsa a lokacin rikicin kabilanci.

A cikin jawabin ta daga Amurka, Mataimakiyar Sakataren Gwamnatin Majalisar Dinkin Duniya, Amina Mohammed, ta ce wannan shiri zai samar da yanayi mai kyau ga yara su koyi ilimi da kuma taimaka wa iyalai su samu ci gaba.

Previous Post

Fashewar Bututun Gas na Escravos zuwa Lagos, NNPC Ta Dauki Matakin Gaggawa a Jihar Delta

Next Post

Matsalar da ke janyo yawan ɓarin ciki da mata ba su sani ba

Related Posts

Hon. Samaila Aliyu Makarfi Ya Taya Sanata Aminu Waziri Tambuwal Murnar Cikar Shekaru 60 da Haihuwa
Labarai

Hon. Samaila Aliyu Makarfi Ya Taya Sanata Aminu Waziri Tambuwal Murnar Cikar Shekaru 60 da Haihuwa

January 11, 2026
Dangote Ya Janye Korafi Akan Tsohon Shugaban NMDPRA, Amma ICPC Ta Ce Bincike Zai Ci Gaba
Labarai

Dangote Ya Janye Korafi Akan Tsohon Shugaban NMDPRA, Amma ICPC Ta Ce Bincike Zai Ci Gaba

January 8, 2026
Labarai

Dangote Cement Na Taimakawa Al’ummomin Benue Ta Hanyar Ayyuka Masu Ma’ana inji Gwamnatin Tarayya

January 7, 2026
2026 Hajji: Shugaban NAHCON ya tafi Saudiyya domin kammala shirye-shirye
Labarai

2026 Hajji: Shugaban NAHCON ya tafi Saudiyya domin kammala shirye-shirye

January 4, 2026
Sakon Sabuwar Shekara
Labarai

Sakon Sabuwar Shekara

January 2, 2026
Gwamna Namadi Ya Amince da Nadin Jami’ai 27 Don Taimakawa Aikin Hajjin 2026 a Jigawa
Labarai

Gwamna Namadi Ya Amince da Nadin Jami’ai 27 Don Taimakawa Aikin Hajjin 2026 a Jigawa

December 31, 2025
Next Post
Matsalar da ke janyo yawan ɓarin ciki da mata ba su sani ba

Matsalar da ke janyo yawan ɓarin ciki da mata ba su sani ba

Matan da suka fi shahara a 2025

Matan da suka fi shahara a 2025

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Trending
  • Comments
  • Latest
“Siyan wayoyin hannu na zuwa da babbar matsala” — Abubakar Ubale

“Siyan wayoyin hannu na zuwa da babbar matsala” — Abubakar Ubale

January 1, 2026
ADC ta samu babban jigo na siyasa Farfesa Sani Bello don aikin duba kundin tsarin mulki bayan Awanni 24 da barin APC

ADC Ta Nuna Sabuwar Zamanin Gaskiya da Aminci ta Hanyar Nada Farfesa Mohammed Sani Bell

January 8, 2026
Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta bukaci kungiyoyin likitocin jihohi da su bi ka’idojin kiwon lafiya na aikin Hajjin 2026 da Saudiyya ta fitar da tsattsauran ra’ayi.

Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta bukaci kungiyoyin likitocin jihohi da su bi ka’idojin kiwon lafiya na aikin Hajjin 2026 da Saudiyya ta fitar da tsattsauran ra’ayi.

December 30, 2025
Gwamnan Osun, Masana Ilimi da Sarakunan Gargajiya Za Su Halarci Bikin Cika Shekaru 40 na KIDVARC

Gwamnan Osun, Masana Ilimi da Sarakunan Gargajiya Za Su Halarci Bikin Cika Shekaru 40 na KIDVARC

November 26, 2025
Sanata Anthony Yaro Ya Gamsu Da Dokar Cin Zarafin yara

Sanata Anthony Yaro Ya Gamsu Da Dokar Cin Zarafin yara

0
Zamu Fara Bincike A Kan Matuka Jiragen Sama Don Hanasu Shan Kayan Maye, Inji Sanata Buhari Abdulfatah

Zamu Fara Bincike A Kan Matuka Jiragen Sama Don Hanasu Shan Kayan Maye, Inji Sanata Buhari Abdulfatah

0
Kudirin Dokar Cibiyar Hukumar EFCC Ta Tsallake karatu Na Biyu

Kudirin Dokar Cibiyar Hukumar EFCC Ta Tsallake karatu Na Biyu

0
Yan Majalisa da Ma’aikatar Yan Sanda sun goyi bayan kashi 15% na Mata Wurin daukar aiki

Yan Majalisa da Ma’aikatar Yan Sanda sun goyi bayan kashi 15% na Mata Wurin daukar aiki

0
Yadda ƴaƴan cashew ke rage ƙiba da haɗarin kamuwa da ciwon zuciya

Yadda ƴaƴan cashew ke rage ƙiba da haɗarin kamuwa da ciwon zuciya

January 15, 2026
Hon. Samaila Aliyu Makarfi Ya Taya Sanata Aminu Waziri Tambuwal Murnar Cikar Shekaru 60 da Haihuwa

Hon. Samaila Aliyu Makarfi Ya Taya Sanata Aminu Waziri Tambuwal Murnar Cikar Shekaru 60 da Haihuwa

January 11, 2026
ADC ta samu babban jigo na siyasa Farfesa Sani Bello don aikin duba kundin tsarin mulki bayan Awanni 24 da barin APC

ADC Ta Nuna Sabuwar Zamanin Gaskiya da Aminci ta Hanyar Nada Farfesa Mohammed Sani Bell

January 8, 2026
Dangote Ya Janye Korafi Akan Tsohon Shugaban NMDPRA, Amma ICPC Ta Ce Bincike Zai Ci Gaba

Dangote Ya Janye Korafi Akan Tsohon Shugaban NMDPRA, Amma ICPC Ta Ce Bincike Zai Ci Gaba

January 8, 2026

Recent News

Yadda ƴaƴan cashew ke rage ƙiba da haɗarin kamuwa da ciwon zuciya

Yadda ƴaƴan cashew ke rage ƙiba da haɗarin kamuwa da ciwon zuciya

January 15, 2026
Hon. Samaila Aliyu Makarfi Ya Taya Sanata Aminu Waziri Tambuwal Murnar Cikar Shekaru 60 da Haihuwa

Hon. Samaila Aliyu Makarfi Ya Taya Sanata Aminu Waziri Tambuwal Murnar Cikar Shekaru 60 da Haihuwa

January 11, 2026
ADC ta samu babban jigo na siyasa Farfesa Sani Bello don aikin duba kundin tsarin mulki bayan Awanni 24 da barin APC

ADC Ta Nuna Sabuwar Zamanin Gaskiya da Aminci ta Hanyar Nada Farfesa Mohammed Sani Bell

January 8, 2026
Dangote Ya Janye Korafi Akan Tsohon Shugaban NMDPRA, Amma ICPC Ta Ce Bincike Zai Ci Gaba

Dangote Ya Janye Korafi Akan Tsohon Shugaban NMDPRA, Amma ICPC Ta Ce Bincike Zai Ci Gaba

January 8, 2026
Kasuwancin Duniya

© 2025 Kasuwancin Duniya - Wanda ya tsara AuspiceWeb.

Kewaya Site

  • Gida
  • Game da Mu
  • Tuntuɓar
  • Advertise
  • Privacy & Policy

Biyo Mu

No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni

© 2025 Kasuwancin Duniya - Wanda ya tsara AuspiceWeb.

Powered by
...
►
Necessary cookies enable essential site features like secure log-ins and consent preference adjustments. They do not store personal data.
None
►
Functional cookies support features like content sharing on social media, collecting feedback, and enabling third-party tools.
None
►
Analytical cookies track visitor interactions, providing insights on metrics like visitor count, bounce rate, and traffic sources.
None
►
Advertisement cookies deliver personalized ads based on your previous visits and analyze the effectiveness of ad campaigns.
None
►
Unclassified cookies are cookies that we are in the process of classifying, together with the providers of individual cookies.
None
Powered by