• Gida
  • Game da Mu
  • Tuntuɓar
  • Advertise
  • Privacy & Policy
Kasuwancin Duniya
Advertisement
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
No Result
View All Result
Kasuwancin Duniya
No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
  • Al’adu da Fasaha
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
Home Labarai

Matatar Dangote Ta Soki Karin Farashin Man Fetur Sama da ₦739/Lita a Fadin Kasa

Ta Gargadi Masu Kirkirar Karancin Man, Ta Bukaci 'Yan Najeriya Su Kai Rahoton Tashoshin MRS da Ba Su Bin Ka'ida Ba

December 22, 2025
in Labarai
Reading Time: 2 mins read
0
Matatar Dangote Ta Soki Karin Farashin Man Fetur Sama da ₦739/Lita a Fadin Kasa
0
SHARES
15
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsApp

Daga Ahmed Ahmed

Matatar Man Fetur ta Dangote ta fara sayar da Man Fetur (PMS) a fadin Najeriya a farashin ₦739 kowace lita a dukkan tashoshin mai na MRS Oil Nigeria Plc.

Karanta HakananPosts

Hon. Samaila Aliyu Makarfi Ya Taya Sanata Aminu Waziri Tambuwal Murnar Cikar Shekaru 60 da Haihuwa

Dangote Ya Janye Korafi Akan Tsohon Shugaban NMDPRA, Amma ICPC Ta Ce Bincike Zai Ci Gaba

Dangote Cement Na Taimakawa Al’ummomin Benue Ta Hanyar Ayyuka Masu Ma’ana inji Gwamnatin Tarayya

Wannan mataki na nuni da babban ci gaba a kokarin matatar wajen samar da mai, mai araha ga yan Najeriya da kuma daidaita kasuwar man fetur a kasa.

Akwai Sama da tashoshin MRS 2,000 a fadin kasa, ana sa ran sabon farashin zai fara aiki a dukkan wuraren, domin tabbatar da cewa ‘yan Najeriya sun amfana da wannan saukin farashi.

A cikin wata sanarwa, matatar ta yaba wa ‘yan kasuwa da suka rungumi sabon tsarin farashi, tare da bukatar sauran su bi sahu domin farfado da tattalin arzikin kasa.

“Muna yaba wa MRS da sauran ‘yan kasuwa da suka nuna kishin kasa ta hanyar saukar da farashin a matakin famfo. Muna kira ga sauran su shiga wannan yunkuri domin tallafa wa farfadowar tattalin arzikin Najeriya,” in ji matatar.

A tarihi, lokutan bukukuwa na da alaka da karancin mai da tashin farashi.

Sai dai Matatar Dangote ta kawo sauyi mai karfi a kasuwa ta hanyar rage farashin famfo a lokacin da yan Najeriya ke fuskantar kalubale. Tare da tabbacin samar da lita miliyan 50 a kowace rana, wannan shiri yana sauya tsarin samar da mai a lokacin bukukuwa.

Ta hanyar tace mai a cikin gida da yawa, matatar na rage dogaro da kasuwannin waje masu sauyin farashi, tana kare Najeriya daga Dogara Akan kudin waje, daidaita darajar Naira, da kuma karfafa tsaron makamashi.

Wannan ci gaba na rage farashi da kuma tabbacin wadatar mai, yana kawo sauki ga gidaje, ‘yan kasuwa, da masu sufuri a fadin kasa.

Matatar Dangote ta kuma fitar da gargadi mai karfi ga masu kokarin kirkirar karancin mai domin hana aiwatar da sabon farashin, tana kira ga hukumomin gwamnati su dauki mataki cikin gaggawa.

“Duk wani yunkuri na kirkirar karancin mai ko hana wadatar sa domin hana aiwatar da sabon farashi ba zai yuwu ba kuma ba za a yarda da shi ba. Muna bukatar hukumomin da ke kula da harkar su kasance cikin shiri su kuma dauki mataki cikin gaggawa, musamman a wannan lokaci na bukukuwa,” in ji sanarwar.

An shawarci masu amfani da mai da su guji sayen mai a farashi mai tsada idan akwai mai, mai inganci da araha a kusa.

“Muna karfafa gwiwar ‘yan Najeriya da su guji sayen PMS a farashi mai tsada idan suna iya samun mai da aka tace a cikin gida a ₦739 kowace lita daga fiye da tashoshin MRS 2,000 a fadin kasa. Ku kai rahoton duk wata tasha ta MRS da ke sayar da mai sama da ₦739 ta kiran lamabr wayan 0800 123 5264,” in ji matatar.

“Muna kuma kira ga sauran masu tashar mai da su sayi kayayyakinmu domin a yada amfanin wannan saukin farashi ga ‘yan Najeriya a dukkan tashoshi, domin samar da sauki mai fadi da kuma daidaita kasuwar man fetur.”

Matatar Man Fetur ta Dangote ta sake jaddada kudirinta na samar da mai cikin lokaci, daidaita farashi, da kuma tabbatar da tsaron makamashi, tana mai cewa ayyukanta na dogara ne da muradun kasa na dogon lokaci, ba matsin lamba na kasuwa na gajeren lokaci ba.

“Manufarmu ta kasance a bayyane, tabbatar da wadatar kayayyakin man fetur masu inganci a farashi mai sauki ga ‘yan Najeriya, tare da tallafa wa daidaiton tattalin arziki da rage dogaro da shigo da kaya daga waje,” in ji matatar a karshe.

Previous Post

Shugaban Hukumar Jin Dadin Alhazzai ta Kasa (NAHCON) ya gana da jami’an Ma’aikatar Aikin Hajj da Umrah ta kasar Saudiya

Next Post

Kamfanin Dangote Cement ta Kaddamar da Shirye shiryen Tallafin Al’umma da Darajarsu Ta Kai Miliyoyin Naira a Al’ummomin Gboko

Related Posts

Hon. Samaila Aliyu Makarfi Ya Taya Sanata Aminu Waziri Tambuwal Murnar Cikar Shekaru 60 da Haihuwa
Labarai

Hon. Samaila Aliyu Makarfi Ya Taya Sanata Aminu Waziri Tambuwal Murnar Cikar Shekaru 60 da Haihuwa

January 11, 2026
Dangote Ya Janye Korafi Akan Tsohon Shugaban NMDPRA, Amma ICPC Ta Ce Bincike Zai Ci Gaba
Labarai

Dangote Ya Janye Korafi Akan Tsohon Shugaban NMDPRA, Amma ICPC Ta Ce Bincike Zai Ci Gaba

January 8, 2026
Labarai

Dangote Cement Na Taimakawa Al’ummomin Benue Ta Hanyar Ayyuka Masu Ma’ana inji Gwamnatin Tarayya

January 7, 2026
2026 Hajji: Shugaban NAHCON ya tafi Saudiyya domin kammala shirye-shirye
Labarai

2026 Hajji: Shugaban NAHCON ya tafi Saudiyya domin kammala shirye-shirye

January 4, 2026
Sakon Sabuwar Shekara
Labarai

Sakon Sabuwar Shekara

January 2, 2026
Gwamna Namadi Ya Amince da Nadin Jami’ai 27 Don Taimakawa Aikin Hajjin 2026 a Jigawa
Labarai

Gwamna Namadi Ya Amince da Nadin Jami’ai 27 Don Taimakawa Aikin Hajjin 2026 a Jigawa

December 31, 2025
Next Post
Kamfanin Dangote Cement ta Kaddamar da Shirye shiryen Tallafin Al’umma da Darajarsu Ta Kai Miliyoyin Naira a Al’ummomin Gboko

Kamfanin Dangote Cement ta Kaddamar da Shirye shiryen Tallafin Al’umma da Darajarsu Ta Kai Miliyoyin Naira a Al’ummomin Gboko

NNPC Ltd Ta Sake Jaddada Kudurinta na Zaman Lafiya da Ci Gaban Makamashi Mai Dorewa a Ogoniland

NNPC Ltd Ta Sake Jaddada Kudurinta na Zaman Lafiya da Ci Gaban Makamashi Mai Dorewa a Ogoniland

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Trending
  • Comments
  • Latest
“Siyan wayoyin hannu na zuwa da babbar matsala” — Abubakar Ubale

“Siyan wayoyin hannu na zuwa da babbar matsala” — Abubakar Ubale

January 1, 2026
ADC ta samu babban jigo na siyasa Farfesa Sani Bello don aikin duba kundin tsarin mulki bayan Awanni 24 da barin APC

ADC Ta Nuna Sabuwar Zamanin Gaskiya da Aminci ta Hanyar Nada Farfesa Mohammed Sani Bell

January 8, 2026
Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta bukaci kungiyoyin likitocin jihohi da su bi ka’idojin kiwon lafiya na aikin Hajjin 2026 da Saudiyya ta fitar da tsattsauran ra’ayi.

Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta bukaci kungiyoyin likitocin jihohi da su bi ka’idojin kiwon lafiya na aikin Hajjin 2026 da Saudiyya ta fitar da tsattsauran ra’ayi.

December 30, 2025
Gwamnan Osun, Masana Ilimi da Sarakunan Gargajiya Za Su Halarci Bikin Cika Shekaru 40 na KIDVARC

Gwamnan Osun, Masana Ilimi da Sarakunan Gargajiya Za Su Halarci Bikin Cika Shekaru 40 na KIDVARC

November 26, 2025
Sanata Anthony Yaro Ya Gamsu Da Dokar Cin Zarafin yara

Sanata Anthony Yaro Ya Gamsu Da Dokar Cin Zarafin yara

0
Zamu Fara Bincike A Kan Matuka Jiragen Sama Don Hanasu Shan Kayan Maye, Inji Sanata Buhari Abdulfatah

Zamu Fara Bincike A Kan Matuka Jiragen Sama Don Hanasu Shan Kayan Maye, Inji Sanata Buhari Abdulfatah

0
Kudirin Dokar Cibiyar Hukumar EFCC Ta Tsallake karatu Na Biyu

Kudirin Dokar Cibiyar Hukumar EFCC Ta Tsallake karatu Na Biyu

0
Yan Majalisa da Ma’aikatar Yan Sanda sun goyi bayan kashi 15% na Mata Wurin daukar aiki

Yan Majalisa da Ma’aikatar Yan Sanda sun goyi bayan kashi 15% na Mata Wurin daukar aiki

0
Yadda ƴaƴan cashew ke rage ƙiba da haɗarin kamuwa da ciwon zuciya

Yadda ƴaƴan cashew ke rage ƙiba da haɗarin kamuwa da ciwon zuciya

January 15, 2026
Hon. Samaila Aliyu Makarfi Ya Taya Sanata Aminu Waziri Tambuwal Murnar Cikar Shekaru 60 da Haihuwa

Hon. Samaila Aliyu Makarfi Ya Taya Sanata Aminu Waziri Tambuwal Murnar Cikar Shekaru 60 da Haihuwa

January 11, 2026
ADC ta samu babban jigo na siyasa Farfesa Sani Bello don aikin duba kundin tsarin mulki bayan Awanni 24 da barin APC

ADC Ta Nuna Sabuwar Zamanin Gaskiya da Aminci ta Hanyar Nada Farfesa Mohammed Sani Bell

January 8, 2026
Dangote Ya Janye Korafi Akan Tsohon Shugaban NMDPRA, Amma ICPC Ta Ce Bincike Zai Ci Gaba

Dangote Ya Janye Korafi Akan Tsohon Shugaban NMDPRA, Amma ICPC Ta Ce Bincike Zai Ci Gaba

January 8, 2026

Recent News

Yadda ƴaƴan cashew ke rage ƙiba da haɗarin kamuwa da ciwon zuciya

Yadda ƴaƴan cashew ke rage ƙiba da haɗarin kamuwa da ciwon zuciya

January 15, 2026
Hon. Samaila Aliyu Makarfi Ya Taya Sanata Aminu Waziri Tambuwal Murnar Cikar Shekaru 60 da Haihuwa

Hon. Samaila Aliyu Makarfi Ya Taya Sanata Aminu Waziri Tambuwal Murnar Cikar Shekaru 60 da Haihuwa

January 11, 2026
ADC ta samu babban jigo na siyasa Farfesa Sani Bello don aikin duba kundin tsarin mulki bayan Awanni 24 da barin APC

ADC Ta Nuna Sabuwar Zamanin Gaskiya da Aminci ta Hanyar Nada Farfesa Mohammed Sani Bell

January 8, 2026
Dangote Ya Janye Korafi Akan Tsohon Shugaban NMDPRA, Amma ICPC Ta Ce Bincike Zai Ci Gaba

Dangote Ya Janye Korafi Akan Tsohon Shugaban NMDPRA, Amma ICPC Ta Ce Bincike Zai Ci Gaba

January 8, 2026
Kasuwancin Duniya

© 2025 Kasuwancin Duniya - Wanda ya tsara AuspiceWeb.

Kewaya Site

  • Gida
  • Game da Mu
  • Tuntuɓar
  • Advertise
  • Privacy & Policy

Biyo Mu

No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni

© 2025 Kasuwancin Duniya - Wanda ya tsara AuspiceWeb.

Powered by
...
►
Necessary cookies enable essential site features like secure log-ins and consent preference adjustments. They do not store personal data.
None
►
Functional cookies support features like content sharing on social media, collecting feedback, and enabling third-party tools.
None
►
Analytical cookies track visitor interactions, providing insights on metrics like visitor count, bounce rate, and traffic sources.
None
►
Advertisement cookies deliver personalized ads based on your previous visits and analyze the effectiveness of ad campaigns.
None
►
Unclassified cookies are cookies that we are in the process of classifying, together with the providers of individual cookies.
None
Powered by