
Daga Bashir Bello, Abuja
Kungiyar ‘Yan Jaridar Wasanni ta Najeriya SWAN ta rattaba hannu kan wata yarjejeniya ta musamman da Kamfanin Byblos Travels and Tours Nigeria Limited, domin samar da rahusa wajen zirga-zirga da kuma tallafin ayyukan tafiya ga ‘yan jaridar wasanni.
An rattaba hannu kan wannan Memorandum of Understanding MoU ne a Abuja. Ana sa ran yarjejeniyar za ta rage nauyin kudi ga ‘yan jarida ta hanyar rahusa tikitin jiragen sama, shawara kan visa, tallafin masauki da sauran fa’idodin da suka shafi tafiye-tafiye.
Da yake jawabi, Shugaban SWAN na Kasa, Mr. Isaiah Benjamin, ya ce wannan yarjejeniya babban mataki ne na inganta jin dadin ‘ya’ya da kuma karfafa sana’ar su.

Shugaban ya ce shugabancin sun yi nazari sosai kan dukkan sharuddan yarjejeniyar kafin amincewa da ita, yayin da ya yaba da wani gogaggen dan jaridar wasanni, Abdulgafar Oladimeji, bisa kokarinsa na kawo wannan yarjejeniya.
“Duk wata al’amari da zai amfana da ‘ya’yan mu, muna sha’awar sa. Bayan karanta abubuwan da ke cikin wannan yarjejeniya, na yi imanin za ta taimaki ‘ya’yan mu matuka” in ji shi.

Benjamin ya tuna da hadarin da ke tattare da tafiya ta hanya da kuma tsadar tikitin jiragen sama na cikin gida a Najeriya. Ya ce saboda haka ne ‘yan jaridar wasanni da yawa ba su iya zuwa wasu muhimman gasa ba.
“Za ku iya tunanin ‘ya’yan mu na tafiya awa goma sha uku ko goma sha hudu ta hanya ne kawai domin su rufe wasa, saboda ba su da kudin tikitin jirgi. Wasu ma sai su daina zuwa gaba daya” in ji shi.
Ya bayyana kyakkyawan fata cewa wannan hadin gwiwa zai ba da dama ga ‘yan jarida da yawa su halarci manyan gasa, ciki har da Gasar Cin Kofin Duniya ta FIFA 2026, Wasannin Commonwealth na Glasgow da kuma Gasar Cin Kofin Mata na Afrika WAFCON.
A nasa bangaren, shugaban tawagar Byblos, Mr. Abubakar Nasrudeen, ya ce kamfanin na farin ciki da hadin gwiwa da SWAN domin saukaka da rage kudin tafiye-tafiyen ‘yan jaridar wasanni na Najeriya na cikin gida da na wajen kasa.
Ya ce kamfanin wanda ya kware wajen siyar da tikiti, hada-hadar visa da shirya yawon bude ido, zai baiwa ‘ya’yan SWAN tayin tafiye-tafiye na musamman wadanda ba a samu su a kasuwa gaba daya ba.

“Mun shirya ba SWAN dukkan tallafin da ya kamata dangane da tikitin jirgi, visa da fakitin tafiya. Muna son ‘ya’ya su ji dadin farashi da dama na musamman da ba za su iya samu a wani wuri ba cikin sauki*” in ji shi.
Nasrudeen ya kara da cewa kamfanin zai ci gaba da neman wasu damammaki a fannin tafiye-tafiye da za su amfana da ‘ya’yan kungiyar.
A nasa bangaren, tsohon Sakataren SWAN na Jihar Kano, Mr. Abdulgafar Oladimeji, wanda ya dauki nauyin kawo wannan hadin gwiwa, ya yaba da shugabancin Shugaban SWAN bisa rungumar duk wata dama da ke inganta walwalar ‘ya’ya da karfafa sana’ar su.
Ya ce daya daga cikin manyan nasarorin wannan shugabanci shine dawo da zaman lafiya da hadin kai a cikin kungiyar.
“*Yau SWAN muryar daya ce. Kungiyar ta yi zaman lafiya. Mutane da yawa ba su san cewa zaman lafiya da hadin kai sun kai biliyoyin naira ga kowace kungiya ba*” in ji shi.
Oladimeji ya ce wannan shugabanci ya samar da yanayi da ke jawo kamfanoni masu kawo sauyi a rayuwar ‘yan jaridar wasanni a fadin kasar.
Ya kara da cewa daya daga cikin manyan abubuwan da ke jawo mutane sana’ar ‘yan jaridar wasanni shi ne dama da ake samu na tafiya da samun kwarewa a kasashen waje.
Wannan yarjejeniya ta zo ne a daidai lokacin da ake shirin Wasannin Commonwealth na 2026 a Glasgow, WAFCON a Morocco da kuma Gasar Cin Kofin Duniya da ke gudana a Amurka, Kanada da Mexico*.
Ana sa ran wannan hadin gwiwa zai bude sabon babi a ci gaban ‘yan jaridar wasanni na Najeriya ta hanyar inganta zirga-zirgar su, kara halartar manyan gasa da kuma inganta ingancin ruwaiton labaran wasanni a kasar.





















