• Gida
  • Game da Mu
  • Tuntuɓar
  • Advertise
  • Privacy & Policy
Kasuwancin Duniya
Advertisement
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
No Result
View All Result
Kasuwancin Duniya
No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
  • Al’adu da Fasaha
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
Home Kasuwanci

Kungiyar ECOWAS Ta Naɗa Dangote Shugaban Majalisar Kasuwanci Don Bunƙasa Tattalin Arziki

December 11, 2025
in Kasuwanci
Reading Time: 4 mins read
0
Kungiyar ECOWAS Ta Naɗa Dangote Shugaban Majalisar Kasuwanci Don Bunƙasa Tattalin Arziki
0
SHARES
11
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsApp

Daga Bashir Bello, Majalisa Abuja.

Ƙungiyar Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) ta sanar da shirin haɗin gwiwa da fitaccen ɗan kasuwa na Afirka, Aliko Dangote, da sauran ɓangarorin masu zaman kansu domin ƙarfafa daidaiton kuɗi da ƙarfin tattalin arziki a yankin.

Karanta HakananPosts

“Siyan wayoyin hannu na zuwa da babbar matsala” — Abubakar Ubale

“Dole ne mutum ya kasance mai taka-tsantsan da haƙuri kafin yin kasuwancin waya” — Abba

Ana Sayar da Fetur akan Naira 739 Kowace Lita a Gidajen Mai Na MRS

Shugaban Hukumar ECOWAS, Omar Touray, ne ya bayyana wannan shiri a zaman taron ministocin ECOWAS karo na 95 da aka gudanar a Abuja ranar Laraba.

Touray ya bayyana cewa an zaɓi Dangote a matsayin shugaban farko na Majalisar Kasuwanci ta ECOWAS, wata sabuwar dandalin da aka ƙirƙira domin jawo jari daga ɓangaren masu zaman kansu da kuma tallafa wa haɗin gwiwar tattalin arzikin yankin.

Ya ce: “Muna ci gaba da aiwatar da Majalisar Kasuwanci ta ECOWAS. Mun zaɓi Alhaji Aliko Dangote a matsayin shugaban farko na wannan majalisa saboda ƙwarewarsa da gogewarsa a harkokin kasuwanci a cikin yankinmu, Africa da ma fadin Duniya.

“Ta wannan majalisa, muna fatan haɗa ɓangarorin masu zaman kansu domin tattauna haɗin gwiwar tattalin arziki da ci gaban yankinmu.

“Majalisar Kasuwanci za ta bunkasa tattaunawa da haɗin gwiwa tsakanin ɓangaren masu zaman kansu, gwamnatoci da hukumomin ECOWAS.”

Hukumar ECOWAS na ƙoƙarin rage dogaro da jari daga ƙasashen waje ta hanyar ƙarfafa zuba jari a tsakanin ƙasashen yankin.

Touray ya ce: “Wannan sha’awar zuba jari a cikin yankinmu na nuna muhimmancin tara jari daga cikinmu domin gina al’ummarmu maimakon jiran jari daga ƙasashen waje da ba su da tabbas.

“Ina da tabbacin cewa da irin jarin da muka gani daga irin su Alhaji Dangote, ɓangaren masu zaman kansu na yankinmu na iya jagorantar ci gaban al’ummarmu idan aka ba su dama da ƙarfafawa.”

Ya kuma bayyana damuwa kan matsalolin da ke fuskantar kasuwar wutar lantarki ta ECOWAS, yana mai cewa: “Wannan dandali ne na kasuwar wutar lantarki ta yankinmu da ke fuskantar ƙalubale saboda bashin da kamfanonin wutar lantarki na ƙasa ke bin sa.”

Ya bukaci ƙasashen mambobi su tallafa wajen dawo da waɗannan bashi a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin ƙarfafa tattalin arzikin yankin.

Baya ga jawo ɓangaren masu zaman kansu, jawabin Touray ya tabo batutuwan da suka shafi juriyar yankin, haɗin kuɗi da ƙirƙirar rundunar yankin don yaƙi da ta’addanci.

An kuma gabatar da sabbin bayanai kan shirin aiki na shekara, kasafin kuɗi da binciken asusun hukumomin ECOWAS domin tantancewa.

Ya ce: “Muna fatan tattaunawarku kan batutuwan da ke gaban wannan taro za su buɗe hanya ga yankin da ke dogaro da kansa, ba tare da rinjayar waje ba ko fuskantar girgizar tattalin arziki daga waje.”

Ministan Harkokin Wajen Saliyo kuma Shugaban Majalisar Ministocin ECOWAS, Timothy Kabba, ya bukaci ƙasashen Yammacin Afirka da su ƙarfafa haɗin kai wajen fuskantar ƙalubalen tsaro, tattalin arziki da dimokuraɗiyya.

A lokacin buɗe taron, Kabba ya ce: “Wannan taro yana ƙara tabbatar da jajircewarmu ga haɗin gwiwar yankin, bisa hangen nesanmu na Yammacin Afirka da kuma mai bunƙasa.”

Ya ce a cikin kwanaki biyu na taron, ministoci za su duba rahotanni da takardun shawarwari da nufin inganta haɗin gwiwar tattalin arziki da siyasa a cikin al’umma.

Yayin bikin cika shekaru 50 da rattaba hannu kan yarjejeniyar Lagos, wanda ya kafa ECOWAS, Kabba ya jaddada muhimmancin haɗin gwiwa tattalin arziki.

Ya ce: “Dole ne mu ci gaba da ƙoƙari wajen samar da yanayi mai kyau ga bunƙasar ɓangaren masu zaman kansu, wanda shi ne ginshiƙin ajandar haɗin tattalin arziki.”

Ya kuma bukaci ƙarin cinikayya a tsakanin ƙasashen yankin, inganta hanyoyin sufuri da haɗin wutar lantarki, da kuma cikakken amfani da yarjejeniyar cinikayya ta Afirka (AfCFTA) domin bunƙasa yankin.

Shugaban ya kuma tabo batutuwan tsaro da ke addabar Yammacin Afirka, ciki har da ta’addanci, tsattsauran ra’ayi, laifukan ƙungiyoyi da sauya gwamnati ba bisa ƙa’ida ba.

Ya jaddada cewa: “Bai kamata kowace ƙasa ta fuskanci waɗannan ƙalubale ita kaɗai ba. Sai ta hanyar ƙarfafa haɗin kai da fahimtar juna tsakanin ƙasashenmu za mu iya shawo kansu.”

Ya bukaci a zuba jari a shirye-shiryen zaman lafiya da tsaro, haɗin gwiwar leƙen asiri da kuma ƙaddamar da Rundunar Tsaro ta ECOWAS.

Kabba ya la’anci juyin mulki da aka yi a wasu ƙasashen yankin, yana mai cewa: “Al’ummarmu dole ta tsaya tsayin daka wajen kin amincewa da juyin mulki ko duk wani take dokar mulki.”

Ya nuna damuwa kan abubuwan da suka faru a Jamhuriyar Guinea-Bissau da ƙoƙarin juyin mulki a Jamhuriyar Benin, yana mai cewa: “Wannan na barazana ga tsarin mulki, dimokuraɗiyya da ƙimar da ke haɗa mu a matsayin al’umma.”

Ya yaba da yadda ECOWAS ta hanzarta mayar da martani kan rikicin siyasa a Guinea-Bissau, yana mai cewa: “Martaninmu cikin gaggawa da haɗin kai, wanda ya haɗa da tattaunawa cikin gaskiya da buɗaɗɗen zuciya, ya nuna jajircewarmu wajen shawo kan rikicin siyasa da dawo da zaman lafiya da tsarin mulki.”

A ƙarshe, Kabba ya ƙarfafa mambobi da su shiga taron da ƙwazo da fata mai kyau.

A nata jawabin, Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Jakadiya Bianca Odumegwu-Ojukwu, ta ja hankalin mahalarta taron kan ƙalubalen da ke fuskantar yankin.

Ta ce: “Shekarun baya sun shaida rashin daidaito a siyasa da rashin haɗin kai, ciki har da sauya gwamnati ba bisa ƙa’ida ba, jinkirin sauya mulki da rashin tabbas a shugabanci a wasu ƙasashe mambobi.

“Wannan na barazana ga ƙimomin dimokuraɗiyya da muka amince da su, kuma na iya lalata ci gaban da muka samu da wahala.”

Game da haɗin tattalin arziki, Jakadiya Odumegwu-Ojukwu ta jaddada buƙatar ƙarin cinikayya a tsakanin ƙasashen yankin da samar da dama ga matasa.

Ta ce: “Makomar yankinmu na dogara ne da zurfafa cinikayya a tsakaninmu, ƙarfafa sarkar samar da kayayyaki, sauƙaƙa zuba jari da samar da dama ga mutane sama da miliyan 400, musamman matasa yan ƙasa da shekaru 25 da ke da kusan kashi 65 cikin 100 na yawan jama’a. Ba shakka suna dogaro da ECOWAS wajen jagorantar su zuwa ci gaba.”

Ministar ta jaddada muhimmancin rawar da majalisar ke takawa wajen tsara manufofi.

Ta ce: “Takardun da ke gabanku na magana ne kan muhimman batutuwa da suka shafi shugabanci, haɗin tattalin arziki, amsa ga bala’o’i, zaman lafiya da tsaro, noma da ingancin hukumomi.”

Ta Kara da cewa Yammacin Afirka na fuskantar ƙarin rikice-rikicen siyasa da matsalolin tsaro, inda wasu ƙasashen ECOWAS ke fama da juyin mulki, ƙoƙarin juyin mulki da sauyin mulki maras tabbas.

Mali, Nijar da Burkina Faso na ƙarƙashin mulkin soja, yayin da Guinea-Bissau ta shiga wannan rukuni bayan wani shigar sojoji. A ranar Lahadi, an hana wani ƙoƙarin juyin mulki a Jamhuriyar Benin.

Halinda ta ƙara taɓarɓarewa sakamakon tsananta matsalolin jinƙai, inda miliyoyin mutane suka rasa matsugunansu a sassa daban-daban na Mali, Nijar, Najeriya da Burkina Faso.

Previous Post

Rigimar Diflomasiyya: Jerin Sunayen Jakadun Tinubu Ya Haifar Da Cece-kuce Da Mahawara

Next Post

Kudurin Dokar Kafa Hukumar Kula da Ingancin Cibiyoyin Kiwon Lafiya Ya Tsallake Karatu Na Biyu

Related Posts

“Siyan wayoyin hannu na zuwa da babbar matsala” — Abubakar Ubale
Kasuwanci

“Siyan wayoyin hannu na zuwa da babbar matsala” — Abubakar Ubale

January 1, 2026
“Dole ne mutum ya kasance mai taka-tsantsan da haƙuri kafin yin kasuwancin waya” — Abba
Kasuwanci

“Dole ne mutum ya kasance mai taka-tsantsan da haƙuri kafin yin kasuwancin waya” — Abba

December 30, 2025
Ana Sayar da Fetur akan Naira 739 Kowace Lita a Gidajen Mai Na MRS
Kasuwanci

Ana Sayar da Fetur akan Naira 739 Kowace Lita a Gidajen Mai Na MRS

December 26, 2025
Farashin Fetur na Man Dangote da Aka Amince da Shi a Hukumance Shine Naira 739 Kowace Lita a Tashoshin MRS a Fadin Kasar, Ku Kasance Masu Lura
Talla

Farashin Fetur na Man Dangote da Aka Amince da Shi a Hukumance Shine Naira 739 Kowace Lita a Tashoshin MRS a Fadin Kasar, Ku Kasance Masu Lura

December 26, 2025
Shawara 5 da Dangote ya bai wa ƴan Najeriya kan talauci
Kasuwanci

Shawara 5 da Dangote ya bai wa ƴan Najeriya kan talauci

December 11, 2025
Sabbin Buhunan Sikari na Dangote Sun Ja Hankali a Bikin Kasuwanci na Kano
Kasuwanci

Sabbin Buhunan Sikari na Dangote Sun Ja Hankali a Bikin Kasuwanci na Kano

December 9, 2025
Next Post
Kudurin Dokar Kafa Hukumar Kula da Ingancin Cibiyoyin Kiwon Lafiya Ya Tsallake Karatu Na Biyu

Kudurin Dokar Kafa Hukumar Kula da Ingancin Cibiyoyin Kiwon Lafiya Ya Tsallake Karatu Na Biyu

Shawara 5 da Dangote ya bai wa ƴan Najeriya kan talauci

Shawara 5 da Dangote ya bai wa ƴan Najeriya kan talauci

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Trending
  • Comments
  • Latest
“Siyan wayoyin hannu na zuwa da babbar matsala” — Abubakar Ubale

“Siyan wayoyin hannu na zuwa da babbar matsala” — Abubakar Ubale

January 1, 2026
ADC ta samu babban jigo na siyasa Farfesa Sani Bello don aikin duba kundin tsarin mulki bayan Awanni 24 da barin APC

ADC Ta Nuna Sabuwar Zamanin Gaskiya da Aminci ta Hanyar Nada Farfesa Mohammed Sani Bell

January 8, 2026
Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta bukaci kungiyoyin likitocin jihohi da su bi ka’idojin kiwon lafiya na aikin Hajjin 2026 da Saudiyya ta fitar da tsattsauran ra’ayi.

Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta bukaci kungiyoyin likitocin jihohi da su bi ka’idojin kiwon lafiya na aikin Hajjin 2026 da Saudiyya ta fitar da tsattsauran ra’ayi.

December 30, 2025
Gwamnan Osun, Masana Ilimi da Sarakunan Gargajiya Za Su Halarci Bikin Cika Shekaru 40 na KIDVARC

Gwamnan Osun, Masana Ilimi da Sarakunan Gargajiya Za Su Halarci Bikin Cika Shekaru 40 na KIDVARC

November 26, 2025
Sanata Anthony Yaro Ya Gamsu Da Dokar Cin Zarafin yara

Sanata Anthony Yaro Ya Gamsu Da Dokar Cin Zarafin yara

0
Zamu Fara Bincike A Kan Matuka Jiragen Sama Don Hanasu Shan Kayan Maye, Inji Sanata Buhari Abdulfatah

Zamu Fara Bincike A Kan Matuka Jiragen Sama Don Hanasu Shan Kayan Maye, Inji Sanata Buhari Abdulfatah

0
Kudirin Dokar Cibiyar Hukumar EFCC Ta Tsallake karatu Na Biyu

Kudirin Dokar Cibiyar Hukumar EFCC Ta Tsallake karatu Na Biyu

0
Yan Majalisa da Ma’aikatar Yan Sanda sun goyi bayan kashi 15% na Mata Wurin daukar aiki

Yan Majalisa da Ma’aikatar Yan Sanda sun goyi bayan kashi 15% na Mata Wurin daukar aiki

0
Hon. Samaila Aliyu Makarfi Ya Taya Sanata Aminu Waziri Tambuwal Murnar Cikar Shekaru 60 da Haihuwa

Hon. Samaila Aliyu Makarfi Ya Taya Sanata Aminu Waziri Tambuwal Murnar Cikar Shekaru 60 da Haihuwa

January 11, 2026
ADC ta samu babban jigo na siyasa Farfesa Sani Bello don aikin duba kundin tsarin mulki bayan Awanni 24 da barin APC

ADC Ta Nuna Sabuwar Zamanin Gaskiya da Aminci ta Hanyar Nada Farfesa Mohammed Sani Bell

January 8, 2026
Dangote Ya Janye Korafi Akan Tsohon Shugaban NMDPRA, Amma ICPC Ta Ce Bincike Zai Ci Gaba

Dangote Ya Janye Korafi Akan Tsohon Shugaban NMDPRA, Amma ICPC Ta Ce Bincike Zai Ci Gaba

January 8, 2026

Dangote Cement Na Taimakawa Al’ummomin Benue Ta Hanyar Ayyuka Masu Ma’ana inji Gwamnatin Tarayya

January 7, 2026

Recent News

Hon. Samaila Aliyu Makarfi Ya Taya Sanata Aminu Waziri Tambuwal Murnar Cikar Shekaru 60 da Haihuwa

Hon. Samaila Aliyu Makarfi Ya Taya Sanata Aminu Waziri Tambuwal Murnar Cikar Shekaru 60 da Haihuwa

January 11, 2026
ADC ta samu babban jigo na siyasa Farfesa Sani Bello don aikin duba kundin tsarin mulki bayan Awanni 24 da barin APC

ADC Ta Nuna Sabuwar Zamanin Gaskiya da Aminci ta Hanyar Nada Farfesa Mohammed Sani Bell

January 8, 2026
Dangote Ya Janye Korafi Akan Tsohon Shugaban NMDPRA, Amma ICPC Ta Ce Bincike Zai Ci Gaba

Dangote Ya Janye Korafi Akan Tsohon Shugaban NMDPRA, Amma ICPC Ta Ce Bincike Zai Ci Gaba

January 8, 2026

Dangote Cement Na Taimakawa Al’ummomin Benue Ta Hanyar Ayyuka Masu Ma’ana inji Gwamnatin Tarayya

January 7, 2026
Kasuwancin Duniya

© 2025 Kasuwancin Duniya - Wanda ya tsara AuspiceWeb.

Kewaya Site

  • Gida
  • Game da Mu
  • Tuntuɓar
  • Advertise
  • Privacy & Policy

Biyo Mu

No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni

© 2025 Kasuwancin Duniya - Wanda ya tsara AuspiceWeb.

Powered by
...
►
Necessary cookies enable essential site features like secure log-ins and consent preference adjustments. They do not store personal data.
None
►
Functional cookies support features like content sharing on social media, collecting feedback, and enabling third-party tools.
None
►
Analytical cookies track visitor interactions, providing insights on metrics like visitor count, bounce rate, and traffic sources.
None
►
Advertisement cookies deliver personalized ads based on your previous visits and analyze the effectiveness of ad campaigns.
None
►
Unclassified cookies are cookies that we are in the process of classifying, together with the providers of individual cookies.
None
Powered by