• Gida
  • Game da Mu
  • Tuntuɓar
  • Advertise
  • Privacy & Policy
Kasuwancin Duniya
Advertisement
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
No Result
View All Result
Kasuwancin Duniya
No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
  • Al’adu da Fasaha
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
Home Kasuwanci

Shawara 5 da Dangote ya bai wa ƴan Najeriya kan talauci

December 11, 2025
in Kasuwanci
Reading Time: 3 mins read
0
Shawara 5 da Dangote ya bai wa ƴan Najeriya kan talauci
0
SHARES
6
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsApp

Attajirin nan na Afirka Aliko Dangote ya bai wa gwamnatin Najeriya da al’ummarta shawarwari kan yaƙi da talauci, bayan wata ganawa da ya yi da shugaban ƙasar Bola Tinubu a farkon wannan mako.

Daga alƙaluma na baya-baya da hukumar ƙididdiga ta Najeriya ta fitar, kimanin kashi 30.9% na al’ummar Najeriya ne ke rayuwa cikin ƙangin talauci, a cewar Bankin Duniya.

Karanta HakananPosts

“Siyan wayoyin hannu na zuwa da babbar matsala” — Abubakar Ubale

“Dole ne mutum ya kasance mai taka-tsantsan da haƙuri kafin yin kasuwancin waya” — Abba

Ana Sayar da Fetur akan Naira 739 Kowace Lita a Gidajen Mai Na MRS

Hakan na nufin suna rayuwa a ƙasar da dalar Amurka 2.15 a kowace rana.

Bankin Duniya ya bayyana cewa gwamnati na buƙatar samar da sauye-sauyen da suka dace domin shawo kan matsalar talauci da ke ci gaba da yi wa al’umma katutu. Rahoton Bankin ya ce duk da gwamnatin tarayyar ta ce ta fito da wasu shirye-shiryen, to amma ana tafiyar hawainiya wajen aiwatar da su.Aliko Dangote, wanda ya fi kowa arziƙi a Afirka na da dukiyar da kimarta ta kai kimanin dala biliyan 30, bisa rahoton mujallar Forbes, inda ya tara arzikinsa ta hanyar manyan kamfanoninsa na siminti da sukari da takin zamani, sannan a baya-bayan nan katafariyar matatar man fetur.

Attajirin ya nuna damuwarsa kan yadda wasu masu kuɗi da manyan ‘yan kasuwa ke rayuwa ba tare da la’akari da bukatun ƙasa ba.

Ya yi tsokaci kan yadda rayuwar alatu ke karkatar da hankali daga abin da zai kawo ci gaban tattalin arziki da ayyukan yi a ƙasa.Zuba jari maimakon rayuwar alatu
Attajirin ya nuna damuwa kan yadda wasu masu kuɗi da ƴan kasuwa ke kashe kuɗi a kan abin alatu ba tare da la’akari da bukatun ƙasa ba. Ya yi kira ga masu arziƙi da ƴan kasuwa su mayar da kuɗaɗensu zuwa gina masana’antu da samar da ayyukan yi ga jama’a musamman a yankunan da ake bukata.

Ya ce duk wanda yake da kudin sayen motar alfarma ta Rolls-Royce da jiragen sama na alfarma, kamata ya yi ya kafa masana’anta.

Juya arziƙi a Najeriya maimakon ƙasashen wajeDangote ya yi kira da a daina jiran masu zuba jari daga ƙasashen waje, ya ce babu yadda masu zuba jari daga ƙetare za su shigo Najeriya idan masu dukiya a cikin gida ba sa zuba jari a gida.

“Kyakkyawan tsari da shugabanci mai gaskiya da dokoki na gari ne ke janyo masu jarin waje.” in ji shi.

Saboda haka masu kuɗi da ‘yan kasuwa na cikin gida ne ginshiƙin tattalin arzikin ƙasa.

Ya ce masu kuɗi su buɗe masana’antu a yankunansu saboda hakan ne hanyar inganta rayuwar jama’a kuma zai janyo masu zuba jari daga waje.

A rage dogaro da kaya daga waje
Hukumomi a Najeriya na yawan kokawa kan yadda al’umma suka fi mayar da hankali wajen amfani da kayan ƙasashen ƙetare, wani lamari da ya sanya gwamnatin Najeriya ta haramta shigo da wasu kayan da take ganin za a iya sarrafawa a cikin gida.

Dangote ya ce “muna ƙoƙarin ganin mun mayar da Najeriya cibiyar sarrafa abubuwa a Afirka.

“Ƙasasehn Afirka na shigo da kaya, amma muna so ne mu tabbatar cewa muna sarrafa duk abin da muke buƙata a cikin gida.”

A yi koyi da shugabannin baya
Dangote ya yi amfani da misalai na rayuwar shugabannin ƙasa a zamanin mulkin soja, inda ya ce: “A lokacin soja, kowa, duk girman muƙaminsa yana amfani ne da mota samfurin Peugeot 504—shi ne mafi girma. To wane ne kai da za ka hau mota Rolls-Royce?”

“Za ku iya jin dadin ku, amma yana da kyau a dinga yin abubuwa da tsari.”

Ya bayyana cewa idan kana da irin waɗannan kudaɗen kamata ya yi ka kafa masana’anta.

A riƙa biyan haraji yadda ya kamata
Dangote ya ce haraji ne ke gina makarantu, asibitoci da gadojin da ake amfani dasu saboda haka ya kamata masu kuɗi da ƴan kasuwa su riƙa biyan haraji yadda ya kamata

“Gwamnati ita ce babbar mai zuba jari ga duk wani mai kamfani ko ɗan kasuwa saboda haka biyan haraji wajibi ne domin shi ne tushen ci gaban kasa.” in ji shi.

Dangote ya kuma jaddada cewa Najeriya na fuskantar ƙalubale mai girma sakamakon yawan haihuwa, inda ake samun yara miliyan 8.7 duk shekara.

Ya ce wannan yana nuni da cewa akwai buƙatar samar da wutar lantarki da ababen more rayuwa, domin tabbatar da cewa ƙasa na iya ɗaukar wannan ƙaruwa ba tare da matsaloli ba wanda shi ya sa waɗannan shawarwari ke da muhimmanci. Daga:BBC Hausa

Previous Post

Kudurin Dokar Kafa Hukumar Kula da Ingancin Cibiyoyin Kiwon Lafiya Ya Tsallake Karatu Na Biyu

Next Post

Alummar Bagwai da Shanono Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Barau Jibrin a Matsayin Gwamnan Jihar Kano

Related Posts

“Siyan wayoyin hannu na zuwa da babbar matsala” — Abubakar Ubale
Kasuwanci

“Siyan wayoyin hannu na zuwa da babbar matsala” — Abubakar Ubale

January 1, 2026
“Dole ne mutum ya kasance mai taka-tsantsan da haƙuri kafin yin kasuwancin waya” — Abba
Kasuwanci

“Dole ne mutum ya kasance mai taka-tsantsan da haƙuri kafin yin kasuwancin waya” — Abba

December 30, 2025
Ana Sayar da Fetur akan Naira 739 Kowace Lita a Gidajen Mai Na MRS
Kasuwanci

Ana Sayar da Fetur akan Naira 739 Kowace Lita a Gidajen Mai Na MRS

December 26, 2025
Farashin Fetur na Man Dangote da Aka Amince da Shi a Hukumance Shine Naira 739 Kowace Lita a Tashoshin MRS a Fadin Kasar, Ku Kasance Masu Lura
Talla

Farashin Fetur na Man Dangote da Aka Amince da Shi a Hukumance Shine Naira 739 Kowace Lita a Tashoshin MRS a Fadin Kasar, Ku Kasance Masu Lura

December 26, 2025
Kungiyar ECOWAS Ta Naɗa Dangote Shugaban Majalisar Kasuwanci Don Bunƙasa Tattalin Arziki
Kasuwanci

Kungiyar ECOWAS Ta Naɗa Dangote Shugaban Majalisar Kasuwanci Don Bunƙasa Tattalin Arziki

December 11, 2025
Sabbin Buhunan Sikari na Dangote Sun Ja Hankali a Bikin Kasuwanci na Kano
Kasuwanci

Sabbin Buhunan Sikari na Dangote Sun Ja Hankali a Bikin Kasuwanci na Kano

December 9, 2025
Next Post
Alummar Bagwai da Shanono Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Barau Jibrin a Matsayin Gwamnan Jihar Kano

Alummar Bagwai da Shanono Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Barau Jibrin a Matsayin Gwamnan Jihar Kano

Fashewar Bututun Gas na Escravos zuwa Lagos, NNPC Ta Dauki Matakin Gaggawa a Jihar Delta

Fashewar Bututun Gas na Escravos zuwa Lagos, NNPC Ta Dauki Matakin Gaggawa a Jihar Delta

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Trending
  • Comments
  • Latest
“Siyan wayoyin hannu na zuwa da babbar matsala” — Abubakar Ubale

“Siyan wayoyin hannu na zuwa da babbar matsala” — Abubakar Ubale

January 1, 2026
ADC ta samu babban jigo na siyasa Farfesa Sani Bello don aikin duba kundin tsarin mulki bayan Awanni 24 da barin APC

ADC Ta Nuna Sabuwar Zamanin Gaskiya da Aminci ta Hanyar Nada Farfesa Mohammed Sani Bell

January 8, 2026
Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta bukaci kungiyoyin likitocin jihohi da su bi ka’idojin kiwon lafiya na aikin Hajjin 2026 da Saudiyya ta fitar da tsattsauran ra’ayi.

Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta bukaci kungiyoyin likitocin jihohi da su bi ka’idojin kiwon lafiya na aikin Hajjin 2026 da Saudiyya ta fitar da tsattsauran ra’ayi.

December 30, 2025
Gwamnan Osun, Masana Ilimi da Sarakunan Gargajiya Za Su Halarci Bikin Cika Shekaru 40 na KIDVARC

Gwamnan Osun, Masana Ilimi da Sarakunan Gargajiya Za Su Halarci Bikin Cika Shekaru 40 na KIDVARC

November 26, 2025
Sanata Anthony Yaro Ya Gamsu Da Dokar Cin Zarafin yara

Sanata Anthony Yaro Ya Gamsu Da Dokar Cin Zarafin yara

0
Zamu Fara Bincike A Kan Matuka Jiragen Sama Don Hanasu Shan Kayan Maye, Inji Sanata Buhari Abdulfatah

Zamu Fara Bincike A Kan Matuka Jiragen Sama Don Hanasu Shan Kayan Maye, Inji Sanata Buhari Abdulfatah

0
Kudirin Dokar Cibiyar Hukumar EFCC Ta Tsallake karatu Na Biyu

Kudirin Dokar Cibiyar Hukumar EFCC Ta Tsallake karatu Na Biyu

0
Yan Majalisa da Ma’aikatar Yan Sanda sun goyi bayan kashi 15% na Mata Wurin daukar aiki

Yan Majalisa da Ma’aikatar Yan Sanda sun goyi bayan kashi 15% na Mata Wurin daukar aiki

0
Yadda ƴaƴan cashew ke rage ƙiba da haɗarin kamuwa da ciwon zuciya

Yadda ƴaƴan cashew ke rage ƙiba da haɗarin kamuwa da ciwon zuciya

January 15, 2026
Hon. Samaila Aliyu Makarfi Ya Taya Sanata Aminu Waziri Tambuwal Murnar Cikar Shekaru 60 da Haihuwa

Hon. Samaila Aliyu Makarfi Ya Taya Sanata Aminu Waziri Tambuwal Murnar Cikar Shekaru 60 da Haihuwa

January 11, 2026
ADC ta samu babban jigo na siyasa Farfesa Sani Bello don aikin duba kundin tsarin mulki bayan Awanni 24 da barin APC

ADC Ta Nuna Sabuwar Zamanin Gaskiya da Aminci ta Hanyar Nada Farfesa Mohammed Sani Bell

January 8, 2026
Dangote Ya Janye Korafi Akan Tsohon Shugaban NMDPRA, Amma ICPC Ta Ce Bincike Zai Ci Gaba

Dangote Ya Janye Korafi Akan Tsohon Shugaban NMDPRA, Amma ICPC Ta Ce Bincike Zai Ci Gaba

January 8, 2026

Recent News

Yadda ƴaƴan cashew ke rage ƙiba da haɗarin kamuwa da ciwon zuciya

Yadda ƴaƴan cashew ke rage ƙiba da haɗarin kamuwa da ciwon zuciya

January 15, 2026
Hon. Samaila Aliyu Makarfi Ya Taya Sanata Aminu Waziri Tambuwal Murnar Cikar Shekaru 60 da Haihuwa

Hon. Samaila Aliyu Makarfi Ya Taya Sanata Aminu Waziri Tambuwal Murnar Cikar Shekaru 60 da Haihuwa

January 11, 2026
ADC ta samu babban jigo na siyasa Farfesa Sani Bello don aikin duba kundin tsarin mulki bayan Awanni 24 da barin APC

ADC Ta Nuna Sabuwar Zamanin Gaskiya da Aminci ta Hanyar Nada Farfesa Mohammed Sani Bell

January 8, 2026
Dangote Ya Janye Korafi Akan Tsohon Shugaban NMDPRA, Amma ICPC Ta Ce Bincike Zai Ci Gaba

Dangote Ya Janye Korafi Akan Tsohon Shugaban NMDPRA, Amma ICPC Ta Ce Bincike Zai Ci Gaba

January 8, 2026
Kasuwancin Duniya

© 2025 Kasuwancin Duniya - Wanda ya tsara AuspiceWeb.

Kewaya Site

  • Gida
  • Game da Mu
  • Tuntuɓar
  • Advertise
  • Privacy & Policy

Biyo Mu

No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni

© 2025 Kasuwancin Duniya - Wanda ya tsara AuspiceWeb.

Powered by
...
►
Necessary cookies enable essential site features like secure log-ins and consent preference adjustments. They do not store personal data.
None
►
Functional cookies support features like content sharing on social media, collecting feedback, and enabling third-party tools.
None
►
Analytical cookies track visitor interactions, providing insights on metrics like visitor count, bounce rate, and traffic sources.
None
►
Advertisement cookies deliver personalized ads based on your previous visits and analyze the effectiveness of ad campaigns.
None
►
Unclassified cookies are cookies that we are in the process of classifying, together with the providers of individual cookies.
None
Powered by