Hukumar Kula da agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) a ranar Alhamis ta ilimantar da mazauna Jihar Kaduna tare da gudanar da atisayen ceto lokacin ambaliyar ruwa domin ƙarfafa shirye-shiryen al’umma kafin kakar damina ta 2026.

Atisayen na daga cikin Kamfen ɗin Shirye-shirye don wayar da Kan alumma akan Bala’i na NEMA na Shekara ta 2026 kan Ambaliyar da sauran hadurra a faɗin ƙasar.

Mr Suleiman Muhammad, Shugaban Ayyuka na Ofishin NEMA na Kaduna, ya ce manufar atisayen ita ce haɓakawa da wayar da Kan mazauna su zama na farko da za su ba da agajin gaggawa kafin isowar hukumomin ceto.

Muhammad ya ce an tsara atisayen ne domin bai wa al’ummomi ƙwarewar aiki ta gaske kan ceto da taimakon gaggawa, domin rage asarar da ke faruwa a lokacin ambaliyar ruwa.

“Ta hanyar horar da al’ummomi da gudanar da atisaye, za su iya bada taimako na gaggawa nan take idan wani abu ya faru kafin hukumomin gwamnati su iso.

“Muna son al’ummomi su fara ceto mutanensu kafin isowar kowace hukumar agaji,” inji shi.

Ya ce Kaduna na daga cikin jihohin da Hukumar Kula da Yanayi ta Nijeriya da Hukumar Hidimar Ruwa ta Nijeriya suka nuna suna cikin haɗarin Ambaliyar Ruwa na matsakaici a shekarar 2026, bisa tsinkayen da suka yi.

A cewarsa, ƙananan hukumomi ashirin da daya (21) a jihar ne ake tsammanin Ambaliyar zai shafa a lokacin damina.

Muhammad ya ce NEMA ta riga ta gana da masu ruwa da tsaki da sarakunan gargajiya a ƙananan hukumomin Chikun da Kaduna ta Arewa kan matakan tsaro da za a ɗauka domin kaucewa Ambaliyar.
Ya ce hukumar ta kuma ilimantar da al’ummomi kan tsaftace magudanun ruwa da aka toshe da kuma ɗaukar matakan kariya domin rage illar kalubalen Ambaliyar Ruwa.
“Bamu son bala’i ya faru, amma muna son ɗaukar matakan kariya kafin bala’in ya auku domin a rage asarar rayuka da dukiya,” inji shi.
Da yake jawabi ma, Fasto Andrew Gladstone, Babban Mai Kula da wata coci a yankin da lamarin ya shafa, ya yaba wa NEMA da Ƙungiyar Red Cross ta Nijeriya kan atisayen ceto da suka gudanar.
Gladstone ya ce Ambaliyar Ruwa ya zama lamari da ke faruwa akai-akai a yankin, yana faruwa kusan sau biyu a shekara yana jefa mazauna cikin wahala.
“Wannan matsalar Ambaliyar tana faruwa akai-akai, wataƙila sau biyu a shekara, kuma ta haifar mana da ƙalubale da yawa da.”
Zanyi Amfani da wannan damar domin yiwa NEMA da Red cross godiya Akan taimakon da Suke bamu Amma duk da haka mun son Gwamnati ta taimaka don Dakile wannan kalubalen.





















