Gwamnatin Tarayya ta ayyana Alhamis, 19 ga Maris da Juma’a, 20 ga Maris 2026 a matsayin ranakun hutu domin bikin Eid-ul-Fitr, wanda ke nuna ƙarshen watan Ramadan mai tsarki.
Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ya bayyana hakan a madadin Gwamnatin Tarayya cikin wata sanarwa dauke da sa hannun Dr Magdalene Ajani, Babban Sakatare a ma’aikatar, wanda aka fitar a ranar Talata.
Ministan Ya yi fatan alheri tare da taya murna ga al’ummar Musulmi bisa kammala azumin watan Ramadan cikin nasara, tare da kira da su ci gaba da riƙe kyawawan dabi’u na ƙauna, karamci, zaman lafiya, haƙuri, da sadaukarwa da aka jaddada a cikin watan mai tsarki.
Haka kuma ya yi kira ga ‘yan Najeriya su yi amfani da wannan lokacin biki wajen roƙon Allah ya ci gaba da ba wa ƙasar zaman lafiya, haɗin kai, da ci gaba.
Ya tabbatar da cewa Gwamnatin Tarayya tana da cikakken niyya wajen ƙarfafa haɗin kan ƙasa da zaman lafiya tsakanin ‘yan Najeriya.
Ministan yayi Kira ga jama’a su yi bikin cikin natsuwa tare da taimaka ma Masu buƙata a cikin al’umma.





















