Kamfanin NNPC Limited ya samu amincewar Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu GCFR, kan wani muhimmin shirin Bunkasa tattalin arziki da zai kawo zuba jari na kasar waje har Dala Biliyan 20 a aikin Bonga Southwest Aparo (BSWA) deepwater.
Wannan mataki ya zama babbar nasara ga ƙoƙarin Najeriya na jawo manyan jarin duniya da kuma hanzarta ci gaban tattalin arziki mai ɗorewa.
Hakkan na kunshe ne a wata Sanarwa dauke da sa hannun Andy Odeh
Babban Jami’in Hulɗa da Jama’a
NNPC Limited a Abuja.
A cewar Sanarwan, amincewar ta biyo bayan watanni na tattaunawa mai zurfi tsakanin NNPC Limited a matsayin mai lasisi, Hukumar Haraji ta Ƙasa (NRS), Mai Ba da Shawara na Musamman ga Shugaban Ƙasa kan Harkokin Makamashi, Olu Verheijen, da Shugaban Kamfanin Shell, Mr. Wael Sawan. Wannan mataki ya nuna cikakken amincewa da manufofin gwamnati da kuma ƙudirin ta na sauya tsare-tsaren tattalin arziki zuwa sakamakon da ake iya gani.
Shugaban Kamfanin NNPC Limited, Injiniya Bashir Bayo Ojulari, ya bayyana cewa
“Wannan amincewa shaida ce ta jagorancin Shugaban Ƙasa, da kuma yadda NNPC ke gudanar da aiki cikin tsari da ƙwarewa wajen tsara manyan yarjejeniyoyi da ke kawo ƙima ga Najeriya. Aikin Bonga Southwest ya tsaya tsayin daka tsawon kusan shekaru ashirin, amma yau ƙarƙashin jagorancin Shugaba Tinubu da ƙoƙarin NNPC, mun karya wannan shinge.”
Aikin Bonga Southwest zai zama na farko da aka samu amincewar Final Investment Decision (FID) a fannin deepwater tun daga shekarar 2008, wanda zai dawo da matsayin Najeriya a matsayin cibiyar jarin deepwater. Sabon tsarin haraji da Shugaban Ƙasa ya amince da shi ya haɗa da ƙarin rangwamen haraji da kuma warware matsalolin yarjejeniyar 2021, wanda zai tabbatar da daidaito tsakanin ribar masu zuba jari da ƙimar ƙasa.
Ana sa ran aikin zai samar da fiye da aikin yi 5,000 kai tsaye da a kaikaice, tare da samar da gangar mai 150,000 a kowace rana da kuma gas miliyan 140 cubic feet a kowace rana bayan kammalawa. Wannan zai kawo ci gaba mai ɗorewa ga tattalin arzikin ƙasa, ƙara samun kudaden shiga, da tabbatar da tsaron makamashi ga ‘yan Najeriya.




















