
Daga Bashir Bello, Abuja.
Kamfanin Desmims Broadcast Limited, masu mallakar DITV da Alheri Radio, ya samu lambar yabo ta musamman a bikin Nigerian Broadcasting Awards.
Wannan girmamawa yayi nuni ne da gudunmawan da marigayi Khalifa Baba Ahmed yayi a fannin watsa Labarai da aikin jarida. Shi dai marigayi Khalifa Baba Ahmed shine wanda ya kafa tashar, inda aka bayyana irin gudummawar da tashar ke badawa Wajen cigaban kasa
Kungiyar Broadcasting Organisation of Nigeria ce ta shirya wannan lambar yabo domin murnar kwarewar DITV da tasirinta ga al’umma.
Ranar ta kasance cike da farin ciki ga Desmims Broadcast Limited yayin da DITV ta lashe lambar yabo mai daraja daga Nigerian Broadcasting Awards.
Wannan girmamawa ta nuna rawar da tashar ta taka wajen kafa tarihi a masana’antar watsa shirye-shirye a Najeriya.
Bayan karɓar lambar yabo, Shugaban DITV, Dr. Hakeem Baba Ahmed, ya yi kyakkyawan yabo ga marigayi Khalifa Baba Ahmed, yana bayyana shi a matsayin gwarzon watsa shirye-shirye wanda hangen nesansa ya buɗe kofar kafuwar tashoshin talabijin masu zaman kansu a Najeriya.
Ya ce: “A matsayinta na tashar talabijin ta farko mai zaman kanta da ta fara watsa shirye-shirye a Najeriya, DITV ta reni manyan ‘yan jarida kuma ta buɗe ƙofofi ga tashoshin masu zaman kansu. Za mu ci gaba da yin tsari mai kyau, kuma ina kira ga kafafen yada labarai su kasance marasa son kai yayin da zaɓe ke tafe.”
A jawabinsa, Ministan Watsa Labarai da Tsarin Ƙasa, Idris Malagi, ya tabbatar da cewa gwamnatin Shugaba Tinubu za ta ci gaba da tallafawa shirye-shiryen da ke inganta kwarewa a fannin watsa shirye-shirye.
Ya jaddada muhimmancin amfani da ƙarfin kafafen yada labarai wajen ƙarfafa haɗin kan ƙasa.
Ya ce: “Watsa shirye-shirye aiki ne mai inganci da zai iya Kawo Cigaban Alumma da kuma haddin kai. Dole ne mu yi amfani da shi wajen ƙarfafa haɗin kan ƙasa da kuma gina dimokuraɗiyya.”
Sauran wadanda suka samu lambar yabo a daren sun haɗa da Gwamnan Jihar Kaduna Uba Sani, Wanda Kwamishinan yada labarai Ahmed Maiyaki ya wakilta sai kuma Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal Dare, da wasu kungiyoyi da mutane da dama da aka yaba da gudummawarsu ga masana’antar.
Tashar DITV ya Fara watsa shirye shirye a Shekara ta 1994 amatsayin tashar talabijin na farko mai zaman kansa a Najeriya.





















