Daga Bashir Bello, Abuja.
Kamfanin Mai na Ƙasa (NNPC) ya bayyana cewa samar da danyen mai ya ƙaru sosai sakamakon ingantaccen tsaro na bututun mai a yankin Niger Delta.
Shugaban Kamfanin NNPC, Injiniya Bashir Bayo Ojulari, ya ce an samu ƙaruwa daga mafi ƙarancin samarwa na ganga 960,000 a rana a shekarar 2022 zuwa matsakaicin ganga miliyan 1.71 a rana, tare da kololuwa na ganga miliyan 1.84 a shekarar 2025.
Hakkan na kunshe ne a wata Sanarwa dauke da sa hannun Andy Odeh Jami’in Hulda da Jama’a na NNPC Limited.
Acewar Sanarwa, Ojulari ya bayyana haka a taron Majalisar Dokoki kan Tsaron Bututun Mai da aka gudanar a Abuja. Ya ce nasarar ta samo asali ne daga tsarin tsaro na haɗin gwiwa wanda ya haɗa da daidaiton manufofin gwamnati, tattara bayanan sirri, amfani da sojoji, kulawar hukumomin doka, haɗin gwiwar masana’antu, da kuma tsaron al’umma.
Ya jaddada cewa nasarar da aka samu wajen dakile satar mai da lalata bututun mai ta dawo da kwarin gwiwar masu zuba jari a fannin mai da iskar gas na ƙasa.
A jawabinsa, Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, wanda Sanata Jimoh Ibrahim ya wakilta, ya bukaci ƙarin haɗin gwiwa tsakanin hukumomi da masu ruwa da tsaki domin ci gaba da samarwa. Haka kuma, Kakakin Majalisar Wakilai, wanda Jagoran Majalisa, Hon. (Prof.) Julius Ihonvbere ya wakilta, ya bukaci a tabbatar da adalci da daidaito wajen tantance ci gaban da aka samu.
Taron ya samu halartar manyan jami’an tsaro da suka haɗa da Shugaban Sojojin Ƙasa, Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, Darakta Janar na DSS, Kwamandan NSCDC, da kamfanonin tsaro masu zaman kansu.




















