
Daga Bashir Bello, Abuja
Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya ziyarci kuma ya nuna girmamawa ga Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya, Sanata Kashim Shettima, bayan an nada shi a matsayin abokin takar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaben shugaban kasa na shekarar 2027.
Wannan na cikin wata sanarwa da Kakakin Gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Asabar.
A yayin ziyarar da aka kai a daren Juma’a a Gidan Aguda, Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja, Gwamna Yusuf ya taya Mataimakin Shugaban Kasa murna, tare da farin cikinsa bisa wannan nadawa. Ya bayyana nadawar a matsayin karramawa ce ga jajircewarsa da hidimar da yake wa kasa.
Gwamnan ya yi addu’a ga Allah Ya ba Shugaba Tinubu da Mataimakin Shugaba Shettima hikima, lafiya da nasara yayin da suke shirin fuskantar zaben gama-gari na shekarar 2027.
Gwamna Yusuf ya samu rakiyar Dan Majalisar Tarayya mai wakiltar Gwale, Hon. Injiniya Garba Diso; Jami’in Ex-Officio na APC na Kasa, Hon. Muhammad Jamu Yusuf; da Kwamishinan Harkokin Addini na Jihar Kano, Sheikh Ahmad Tijjani Auwalu.
Gwamnan ya sake jaddada goyon bayansa ga dukkan kokarin da ake yi domin inganta hadin kai, zaman lafiya da ci gaba mai dorewa a fadin Najeriya.





















