
Daga Bashir Bello, Abuja
Babban Magoya bayan tsohon Mataimakin Shugaban Kasa Atiku Abubakar, kuma fitaccen jigo a Jam’iyyar African Democratic Congress, ADC, Mai Girma Kamaludeen Skeedo, wanda aka fi sani da Garkuwan Matasa, ya bayyana cewa “babu wurin siyasar jam’iyya” yayin da Najeriya ke kara kusantowa zaben 2027.

Skeedo, wanda ya samu ‘yanci kwanakin baya bayan da Gwamnatin Jihar Kaduna ta tsare shi saboda adawarsa da gwamnatin Gwamna Uba Sani, ya yi wannan jawabi a ranar 30 ga Yuni, 2027.
Ya ce da tsarin da ADC ke da shi yanzu, ko a matakin shugaban kasa ko a jihohin Arewa musamman Jihar Kaduna, jam’iyyar ba za ta iya lashe zabe ba sai an yi manyan gyare-gyare.
“Da yadda ADC ke tafiya yanzu, Atiku Abubakar ba zai iya cin nasara ba sai an yi sauyi. Idan ba a yi gyara ba, to ba shakka za a ce Dana Sani,” in ji Skeedo.
Duk da kasancewarsa daya daga cikin masu suka sosai ga gwamnatin Uba Sani, Skeedo ya ce adawarsa ba ta samo asali daga kiyayya ta mutum ba.
Ya Kara da cewa gwamnan Kaduna yana kokari a wasu fannoni da ake ganin suna kawo sakamakon da alumma ke bukata.
“Gwamnatin Malam Uba Sani tana kokari a wasu abubuwa da nake gani da idona a fili, duk da cewa gwamnatin ta tsare ni ne saboda ina adawa da ita,” in ji shi.
Skeedo ya ce zai ci gaba da kira ga gwamnatin Kaduna da ta gyara kurakurenta domin al’ummar jihar su samu zaman lafiya da ci gaba. Ya jaddada cewa sukar da yake yi ba don raina gwamnan ba ne, sai don tabbatar da an kula da matasan Kaduna yadda ya kamata.
“Idan na samu dama, zan ba Gwamna Malam Uba Sani shawara ta musamman don ci gaban Jihar Kaduna, domin ci gaban jihar shi ne abin da nakeso” in ji shi.
Ya jaddada cewa adawarsa ga gwamnati ba saboda kiyayya ba ce, sai don tura gyare-gyare da inganta rayuwar al’ummar Kaduna, musamman matasa.
Ana ganin Skeedo a matsayin daya daga cikin manyan masu tara matasa na Atiku Abubakar a Kaduna, kuma murya mai karfi a cikin tsarin ADC a jihar.





















