• Gida
  • Game da Mu
  • Tuntuɓar
  • Advertise
  • Privacy & Policy
Kasuwancin Duniya
Advertisement
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
No Result
View All Result
Kasuwancin Duniya
No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
  • Al’adu da Fasaha
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
Home Kasuwanci

Dangote Ya Zamo Gwarzon Tallafawa Ci Gaban Kanana da Matsakaitan Masana’antu a Bikin Kasuwanci na Kano 2025

November 21, 2025
in Kasuwanci
Reading Time: 2 mins read
0
Dangote Ya Zamo Gwarzon Tallafawa Ci Gaban Kanana da Matsakaitan Masana’antu a Bikin Kasuwanci na Kano 2025
0
SHARES
5
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsApp

Daga Ahmed Hassan Ahmed

Rukunin Dangote ya tabbatar da kudurinsa na tallafawa ci gaban tattalin arziki ta hanyar daukar nauyi da kuma halarta a Bikin Kasuwanci na Kasa da Kasa na Kano na shekarar 2025, wanda za a gudanar daga 22 ga Nuwamba zuwa 6 ga Disamba.

Karanta HakananPosts

Dangote Cement, Sinoma Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Dala Biliyan 1 Don Ayyukan Siminti a Fadin Afirka

Rukunin Dangote Ya Haskaka Manufar 2030 a Taron Kasuwanci na Kaduna

Kamfanin Dangote ta Bai wa Abokan Ciniki 50 Kyautar Motoci da Kudi

A cewar Anthony Chiejina, Jami’in Harkokin Sadarwa da Alamarin Kasuwanci na Rukunin, kamfanin ba wai kawai zai dauki nauyin taron ba ne, har ma zai halarta da cikakken shiri don nuna fannonin kasuwancinsa daban-daban. Ana sa ran fiye da kamfanoni 1,000 daga sassa daban-daban na Najeriya da kasashen waje za su halarta.

“Kano cibiyar kasuwanci ce mai matukar muhimmanci a ayyukanmu, kuma tana da matukar tasiri ga harkokin kasuwanci a nahiyar Afirka,” in ji Chiejina, yana jaddada muhimmancin birnin ga hangen nesa na dogon lokaci na kamfanin.

Ya bayyana cewa Kano na dauke da daya daga cikin manyan matatun shinkafa da kamfanin ke ginawa, wanda ke cikin wani shiri mai fadi da ya hada da matatu a jihohin Jigawa, Zamfara, Neja, Kebbi da Sakkwato. Wadannan matatu gaba daya za su iya sarrafa tan miliyan 1.5 na shinkafa a kowace shekara, domin tallafawa kokarin gwamnati na tabbatar da wadatar abinci.

A yayin bikin, rassan kamfanin Dangote za su kafa teburin taimako na musamman domin tattaunawa da mahalarta, tare da bayar da damar fahimtar hanyoyin hadin gwiwa da bunkasa kasuwanci.

Haka kuma, kamfanin zai kaddamar da sabbin nau’ikan kunshin sukari gram 100 da kilo 25 domin biyan bukatun masu amfani da kayayyaki.

Taken bikin bana, Karfafawa Kanana da Matsakaitan Masana’antu Domin Ci Gaba, ya yi daidai da manufar Dangote na inganta ci gaban tattalin arziki mai dorewa da hadin gwiwa.

Fatima Wali-Abdurrahman, Babbar Mai Ba da Shawara kan Ayyuka na Musamman da Huldar ga Shugaban Rukunin, ta bayyana cewa wannan shiri na nufin hada kan kanana da matsakaitan masana’antu da sababbin kasuwanni da abokan hulda.

“Ta hanyar daukar nauyin Bikin Kasuwanci na Kano, muna kokarin karfafawa kanana da matsakaitan masana’antu damar nuna kayayyakinsu, haduwa da abokan hulda da kuma samun sabbin kasuwanni,” in ji ta.

Jakada Hassan Usman Darma, Shugaban Hukumar Kasuwanci, Masana’antu, Ma’adinai da Noma ta Kano (KACCIMA), ya yaba da goyon bayan da Dangote ke bayarwa tun tuni, yana kira kamfanin “babban mai daukar nauyi kuma abokin hadin gwiwa na dabaru.”

Ya bayyana cewa bikin na 2025 zai zo da sabbin gine-gine da fadada wuraren baje koli, wanda zai sa ya zama daya daga cikin mafi girma a tarihi.

“Muna farin cikin zurfafa hadin gwiwarmu da Rukunin Dangote, musamman a fannonin ci gaban SMEs, hadin gwiwar masana’antu da kuma canja wurin fasahar masana’antu,” in ji Darma.

Previous Post

Rigimar Wike da Yerima a Matsayin Gargadi: Dole Shugaba Tinubu Ya Sake Gina Girmar Mulkin Farar Hula Cikin Hankali da Tawali’u

Next Post

Gwamna Idris Ya Nemi Bayani Kan Janye Sojoji Kafin Sace ‘Yan Makaranta Mata

Related Posts

Dangote Cement, Sinoma Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Dala Biliyan 1 Don Ayyukan Siminti a Fadin Afirka
Kasuwanci

Dangote Cement, Sinoma Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Dala Biliyan 1 Don Ayyukan Siminti a Fadin Afirka

February 27, 2026
Rukunin Dangote Ya Haskaka Manufar 2030 a Taron Kasuwanci na Kaduna
Kasuwanci

Rukunin Dangote Ya Haskaka Manufar 2030 a Taron Kasuwanci na Kaduna

February 16, 2026
Kamfanin Dangote  ta Bai wa Abokan Ciniki 50 Kyautar Motoci da Kudi
Kasuwanci

Kamfanin Dangote ta Bai wa Abokan Ciniki 50 Kyautar Motoci da Kudi

February 15, 2026
NDIC Ta Tabbatar da Cikakken Kariya ga Masu Ajiya a Bankuna
Kasuwanci

NDIC Ta Tabbatar da Cikakken Kariya ga Masu Ajiya a Bankuna

February 12, 2026
Taron Baje Kolin Kaduna: Masari da Shugaban KADCCIMA Sun Jaddada Muhimmancin Bunkasa Ci gaban Abubuwan Cikin Gida
Kasuwanci

Taron Baje Kolin Kaduna: Masari da Shugaban KADCCIMA Sun Jaddada Muhimmancin Bunkasa Ci gaban Abubuwan Cikin Gida

February 12, 2026
Dole Africa Ta Daidaita Tsarin Ayyuka, Dokoki da Jarin Kuɗi Don Cimma Tsaron Makamashi Inji Ojulari
Kasuwanci

Dole Africa Ta Daidaita Tsarin Ayyuka, Dokoki da Jarin Kuɗi Don Cimma Tsaron Makamashi Inji Ojulari

February 11, 2026
Next Post
Gwamna Idris Ya Nemi Bayani Kan Janye Sojoji Kafin Sace ‘Yan Makaranta Mata

Gwamna Idris Ya Nemi Bayani Kan Janye Sojoji Kafin Sace ‘Yan Makaranta Mata

Gwamna Radda Ya Halarci Taron G20 Tare da Mataimakin Shugaban Ƙasa Shettima a Afirka Ta Kudu

Gwamna Radda Ya Halarci Taron G20 Tare da Mataimakin Shugaban Ƙasa Shettima a Afirka Ta Kudu

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Trending
  • Comments
  • Latest
“Sayen Wayoyin Hannu Na Zuwa Da Mummunar Matsala” — Abubakar Ubale

“Sayen Wayoyin Hannu Na Zuwa Da Mummunar Matsala” — Abubakar Ubale

January 18, 2026
BA Zamu Sake Yarda ayi Watsi da Matasa Bayan Zabe ba Inji Kungiyar NYA

BA Zamu Sake Yarda ayi Watsi da Matasa Bayan Zabe ba Inji Kungiyar NYA

January 28, 2026
ADC ta samu babban jigo na siyasa Farfesa Sani Bello don aikin duba kundin tsarin mulki bayan Awanni 24 da barin APC

ADC Ta Nuna Sabuwar Zamanin Gaskiya da Aminci ta Hanyar Nada Farfesa Mohammed Sani Bell

January 8, 2026
“Dole ne mutum ya kasance mai taka-tsantsan da haƙuri kafin yin kasuwancin waya” — Abba

“Dole ne mutum ya kasance mai taka-tsantsan da haƙuri kafin yin kasuwancin waya” — Abba

December 30, 2025
Sanata Anthony Yaro Ya Gamsu Da Dokar Cin Zarafin yara

Sanata Anthony Yaro Ya Gamsu Da Dokar Cin Zarafin yara

0
Zamu Fara Bincike A Kan Matuka Jiragen Sama Don Hanasu Shan Kayan Maye, Inji Sanata Buhari Abdulfatah

Zamu Fara Bincike A Kan Matuka Jiragen Sama Don Hanasu Shan Kayan Maye, Inji Sanata Buhari Abdulfatah

0
Kudirin Dokar Cibiyar Hukumar EFCC Ta Tsallake karatu Na Biyu

Kudirin Dokar Cibiyar Hukumar EFCC Ta Tsallake karatu Na Biyu

0
Yan Majalisa da Ma’aikatar Yan Sanda sun goyi bayan kashi 15% na Mata Wurin daukar aiki

Yan Majalisa da Ma’aikatar Yan Sanda sun goyi bayan kashi 15% na Mata Wurin daukar aiki

0
AREWA: Ina Alfaharinmu na Arewa?

AREWA: Ina Alfaharinmu na Arewa?

February 28, 2026
Dangote Cement, Sinoma Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Dala Biliyan 1 Don Ayyukan Siminti a Fadin Afirka

Dangote Cement, Sinoma Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Dala Biliyan 1 Don Ayyukan Siminti a Fadin Afirka

February 27, 2026
Keyamo Ya Gabatar da Tsarin Kasafin Kuɗi na 2026 ₦184.39bn Ga Majalisar Dokoki, Ya Bayyana Nasarorin 2025

Keyamo Ya Gabatar da Tsarin Kasafin Kuɗi na 2026 ₦184.39bn Ga Majalisar Dokoki, Ya Bayyana Nasarorin 2025

February 26, 2026
DHQ Ta Tara Dakarun Afirka Ta Yamma Domin Samar Da Dabarun Yaki Da Ta’addanci

DHQ Ta Tara Dakarun Afirka Ta Yamma Domin Samar Da Dabarun Yaki Da Ta’addanci

February 26, 2026

Recent News

AREWA: Ina Alfaharinmu na Arewa?

AREWA: Ina Alfaharinmu na Arewa?

February 28, 2026
Dangote Cement, Sinoma Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Dala Biliyan 1 Don Ayyukan Siminti a Fadin Afirka

Dangote Cement, Sinoma Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Dala Biliyan 1 Don Ayyukan Siminti a Fadin Afirka

February 27, 2026
Keyamo Ya Gabatar da Tsarin Kasafin Kuɗi na 2026 ₦184.39bn Ga Majalisar Dokoki, Ya Bayyana Nasarorin 2025

Keyamo Ya Gabatar da Tsarin Kasafin Kuɗi na 2026 ₦184.39bn Ga Majalisar Dokoki, Ya Bayyana Nasarorin 2025

February 26, 2026
DHQ Ta Tara Dakarun Afirka Ta Yamma Domin Samar Da Dabarun Yaki Da Ta’addanci

DHQ Ta Tara Dakarun Afirka Ta Yamma Domin Samar Da Dabarun Yaki Da Ta’addanci

February 26, 2026
Kasuwancin Duniya

© 2025 Kasuwancin Duniya - Wanda ya tsara AuspiceWeb.

Kewaya Site

  • Gida
  • Game da Mu
  • Tuntuɓar
  • Advertise
  • Privacy & Policy

Biyo Mu

No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni

© 2025 Kasuwancin Duniya - Wanda ya tsara AuspiceWeb.

Powered by
►
Necessary cookies enable essential site features like secure log-ins and consent preference adjustments. They do not store personal data.
None
►
Functional cookies support features like content sharing on social media, collecting feedback, and enabling third-party tools.
None
►
Analytical cookies track visitor interactions, providing insights on metrics like visitor count, bounce rate, and traffic sources.
None
►
Advertisement cookies deliver personalized ads based on your previous visits and analyze the effectiveness of ad campaigns.
None
►
Unclassified cookies are cookies that we are in the process of classifying, together with the providers of individual cookies.
None
Powered by