
Daga Bashir Bello, Abuja
Za a bude bikin kasuwanci Duniya na Kaduna karo na 47 a ranar 6 ga Fabrairu, 2026, inda ake sa ran Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu zai kaddamar da taron. Wannan shekarar, taken bikin shi ne “Daga Gyare-gyare zuwa Sakamako: Sauyin Tattalin Arziki ta Hanyar Ci gaba da Inganta Kayayyakin Cikin Gida”, tare da Dangote Industries Limited a matsayin babban mai daukar nauyi.
Cibiyar Kasuwanci, Masana’antu, Ma’adinai da Noma ta Kaduna (KADCCIMA) ta bayyana cewa fiye da mutane 10,000 ne ake sa ran za su halarci taron, wanda zai kasance daya daga cikin manyan tarukan kasuwanci a Arewacin Najeriya.
Shugaban KADCCIMA, Alhaji Farouk Suleiman, ya bayyana cewa dangantakar su da rukunin kamfanoni “dangantaka ce da aka gina bisa darajoji na ci gaban masana’antu, bunkasa kayayyakin cikin gida da sauyin tattalin arziki.”
Ya ce biki na bana zai mayar da hankali kan hada kan kamfanoni da hukumomin gwamnati, bunkasa jarin kasuwanci, tallafin kananan masana’antu (SMEs), da samar da damar shiga kasuwa. “Wannan biki na tattalin arziki ne da aka tsara don karfafa cinikayya da kasuwanci, da kuma jawo hankalin masu zuba jari,” in ji shi.
Daraktar, kuma Mai Ba da Shawara ta Musamman ga Shugaban rukunin kamfanoni Dangote, Fatima Wali-Abdurrahman, ta jaddada kudirin kamfanin wajen bunkasa kayayyakin cikin gida.
“Zuba jari na Dangote a bsukari, siminti da sinadarai ya samar da ayyukan yi tare da kara kudin shiga ga gwamnati ta hanyar haraji,” in ji ta.
Ta kara da cewa jarin kamfanin a siminti, noma, takin zamani da man fetur ya nuna yadda zuba jari na cikin gida zai iya sauya tattalin arziki.
Anthony Chiejina, Babban Jami’in Hulda da Jama’a na rukunin kamfanoni Dangote, ya tabbatar cewa kamfanonin da ke karkashin rukunin za su nuna kayayyakin su a bikin. Wadannan sun hada da Dangote Cement, Dangote Sugar, NASCON Allied Industries (Dangote Salt), Dangote-Sinotruk, Dangote Peugeot Automobile, da Dangote Fertiliser.
NASCON zai gabatar da nau’ikan gishiri da kayan yaji, yayin da Dangote Sugar zai nuna dukkan kayayyakin sa. Dangote Cement kuma zai kafa teburin taimako don amsa tambayoyin abokan ciniki.
Wakilan kamfanin za su kasance a shirye don ba da jagora ga masu sha’awar zama dillalai, tare da bayanai kan sharudda da hanyoyin samun wakilci.
Sa’annan KADCCIMA ta bayyana rukunin kamfanoni Dangote a matsayin “tushen ci gaban masana’antu a Najeriya,” tana mai kira ga kamfanin da ya ci gaba da jagoranci ba kawai a matsayin mai daukar nauyi ba, har ma a matsayin mai ba da shawara da abokin ci gaban kananan masana’antu.
Tare da dubban mahalarta da kuma mayar da hankali kan bunkasa kayayyakin cikin gida, bikin kasuwanci na Kaduna na 2026 zai kara karfafa ajandar masana’antu a Najeriya da kuma nuna rawar da kamfanoni masu zaman kansu ke takawa wajen sauya tattalin arziki.





















