Daga Bashir Bello, Abuja
Tare Da bakin ciki da tausayawa, Mai Girma Jakada Dr. Malami Shehu Ma’aji (MFR), Shugaban Kwamitin Shawara na Hukumar Kare Hakkokin Dan Adam ta Duniya (Nigeria), kuma Mai Ba da Shawara na Musamman kan Huldar Gwamnati a Afirka, yayi Ta’aziya ga iyalan marigayi Ibrahim Bunu na Sabon Kaura, Gure a Karamar Hukumar Lere ta Jihar Kaduna wajen jimamin rasuwar ɗansu, Malam Musa Ibrahim, wanda ya riga mu gidan gaskiya a ranar 22 ga Afrilu, 2026.
Malam Musa Ibrahim mutum ne mai kaskantar da kai, gaskiya, da tausayi. Rayuwarsa ta kasance abin koyi na hidima ga ɗan adam, sadaukarwa ga iyali, da kuma kyautatawa ga duk wanda ya haɗu da shi. Ya bayyana marigayin amatsayin Mutum mai son jamaa, hikima, da karamci wanda zaiyi wuya a cike gibin da rasuwarsa zai Kawo.
Acewar sa, Rasuwarsa babban rashi ne ba ga iyalinsa da DSS kaɗai ba, har ma ga al’umma baki ɗaya.
Jakada Dr. Malami Shehu Ma’aji ya miƙa ta’aziyyarsa mafi zurfi ga iyalan yana roƙon Allah Madaukakin Sarki Ya ba su ƙarfin zuciya da juriya a wannan lokacin.
“Allah Ya jikan ruhin Malam Musa Ibrahim da cikakkiyar salama. Amin.” In ji shi.
Mr. Olubayo, a cikin kalaman ta’aziyyarsa, ya kuma shiga cikin jimamin rasuwar marigayin. Ya bayyana tausayinsa ga iyalan marigayi Musa Ibrahim, yana bayyana shi a matsayin mutum mai kyawawan halaye wanda kyautatawarsa suka taɓa rayukan mutane da dama.
Ya yi addu’ar samun ta’aziya da ƙarfin zuciya ga iyalan, da kuma hutu na har abada ga ruhin marigayin.





















