Engr. Muhammed Awal Ibrahim Kwajaffa, ɗan takar Majalisar Wakilai na Mazaɓar Tarayya ta Hawul/Askira, ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da su watsar da nuna halin ko-in-kula a siyasa su shiga fagen domin tsara makomar ƙasar, yana bayyana siyasa a matsayin “injin da ke tafiyar da al’ummomin ɗan adam.”
A cikin wata sanarwa da ya fitar a yau, wacce da kansa ya sanya hannu, Kwajaffa ya ce siyasa ba wasa ne na datti da ya kamata a guje shi ba, Yana mai cewa tsari ne da ke tantance yadda ake rabon albarkatu, damar samun ci gaba, da makomar da za a bar wa manyan gobe.
“Daga matakin ƙasa a kauyukanmu da ƙananan hukumomi har zuwa manyan wuraren yanke shawara na nahiyar, siyasa na nan tana zama harshen ƙarfi. Ana tafiyar da duniya da siyasa ko mun shiga cikinta ko bamu Shiga ba,” inji shi.
Har ila yau, Engr. Kwajaffa yayi gargaɗin cewa nisa da siyasa yana nufin mika ragamar mulki ga wasu. “Waɗanda suka ƙware a ciki ne ke tsara dokoki, suke tattaunawa kan rabon albarkatu…” Inji Kwajaffa.
A cewar Sanarwan, tin farkon mulkin Shugaban Kasa Bola Tinubu yayi namijin kokari Wurin tallafwa matasa ta hanyar Samar da tsare tsare da zasu inganta rayuwan su





















