
A cikin jajircewarta na inganta kiwon lafiya da kuma kawo sauyi mai amfani ga rayuwar ‘yan Najeriya, NNPC Limited ta kaddamar tare da mika dakunan asibiti guda uku da aka gyara gaba ɗaya, kowanne mai gado 100 ga Asibitin Kashi na Ƙasa, Igbobi, Legas.
Aikin, wanda Gidauniyar NNPC Ltd./Gte. ta aiwatar (reshen aikin al’umma na NNPC Limited), ya haɗa da gyaran dakunan G, H, da J. Aikin ya ƙunshi shigar da sabbin gadon marasa lafiya, tsarin iskar likitanci na tsakiya don inganta kulawa, sauya rufin dakuna da silin, sabunta lantarki da injina, da kuma shimfiɗa sabbin bene na vinyl.
Kafin wannan gyara, dakunan sun kasance cikin yanayi mara kyau wanda ya takaita amfani da su, ya kuma rage ƙarfin asibitin wajen karɓar marasa lafiya.
A wajen kaddamarwa, Babban Daraktan Kamfanin, Injiniya Bashir Bayo Ojulari (wanda Akanta Janar Adedapo Segun ya wakilta), ya jaddada cewa ribar NNPC ba ta tsaya ga kuɗi kaɗai ba, har da tasirin zamantakewa da kamfanin ke kawowa. Ya bayyana cewa aikin gyaran ya nuna alfaharin NNPC wajen inganta kiwon lafiya.
Shugabar Gidauniyar NNPC, Emmanuella Arukwe, ta bayyana cewa wannan aiki ya ƙarfafa cibiyar da ta dade tana hidima ga ‘yan Najeriya, tare da nuna rawar da Gidauniyar ke takawa wajen kawo sauye-sauye masu amfani da suka dace da manufofin kiwon lafiya na ƙasa.
Daraktan Asibitin, Dr. Wakeel Lawal, ya nuna godiya matuƙa, yana mai jaddada cewa wannan sauyi ba gyara kaɗai ba ne, illa dai sabuwar fata ce ga marasa lafiya da al’umma.
Taron ya samu halartar Mataimakiyar Shugabar Kamfanin NNPC Ltd. Sashen Ayyukan Kasuwanci, Mrs. Sophia Mbakwe, tare da wakilan al’umma da sarakunan gargajiya. An kuma bayyana farantin tunawa don karrama wannan gagarumin aiki.





















