
Abuja — Babban Jami’in Gudanarwa na Kamfanin Man Fetur na Ƙasa (NNPC Limited), Injiniya Bashir Bayo Ojulari, ya yi kira da a ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin masu ruwa da tsaki a fannin makamashi na Najeriya, yana mai cewa haɗin gwiwa na dabaru shi ne mabuɗin buɗe babbar damar da nahiyar Afirka ke da ita a fannin makamashi, tare da bunƙasa zuba jari, ci gaban masana’antu da dorewar tattalin arziki.
Ojulari ya bayyana hakan ne a ranar Talata yayin gabatar da muhimmin jawabi a wajen buɗe taron NOG Energy Week karo na 25 da aka gudanar a Cibiyar Taro ta Ƙasa ta Bola Ahmed Tinubu da ke Abuja.
A yayin taron, shugaban na NNPC ya kuma gabatar da rahoton shekara guda na ayyukan kamfanin, inda ya bayyana manyan nasarorin da aka samu ta fuskar ayyuka, kasuwanci da harkokin kuɗi cikin shekarar da ta gabata.
Ya bayyana cewa NNPC Ltd ta samu matsakaicin kaso 98 cikin 100 na dawo da ingantaccen aiki a tashoshinta biyar na fitar da ɗanyen mai tsakanin watan Afrilun 2025 da Mayun 2026. Wannan ya nuna gagarumin ci gaba idan aka kwatanta da matsalar da ta taɓa addabar Tashar Bonny Oil and Gas a watan Yunin 2022, lokacin da aikin tashar ya sauka zuwa kusan kaso ɗaya cikin ɗari.
Ojulari ya kuma sanar da cewa yawan ɗanyen man da Najeriya ke hakowa ya kai ganga miliyan 1.71 a kowace rana, wanda shi ne mafi girma cikin shekaru biyar da suka gabata. Haka kuma, kamfanin NNPC Exploration and Production Limited (NEPL) ya kafa sabon tarihi ta hanyar samar da ganga dubu 365 na ɗanyen mai a kullum.
A cewarsa, samar da iskar gas ya kai ƙafar murabba’i biliyan 7.5 a kowace rana, sakamakon kammala aikin ketare Kogin Neja na bututun iskar gas na Ajaokuta-Kaduna-Kano (AKK) da kuma ƙaddamar da Kamfanin Sarrafa Iskar Gas na ANOH.
Ya ƙara da cewa NNPC Ltd ta cika kaso 100 cikin 100 na dukkan wajibcin biyan kuɗaɗen haɗin gwiwar kamfanin (Joint Venture Cash Calls) a duk tsawon shekarar 2025 har zuwa watan Yunin 2026, tare da ci gaba da ƙoƙarin kai yawan haƙar ɗanyen man Najeriya zuwa ganga miliyan biyu a kowace rana.
Da yake bayyana nasarorin kasuwanci, Ojulari ya ce kamfanin ya rattaba hannu kan manyan yarjejeniyoyin sayar da iskar gas (Gas Sale and Purchase Agreements), waɗanda suka haɗa da samar da ƙafar murabba’i biliyan 1.29 na iskar gas a kullum domin ciyar da ayyukan LNG na dogon lokaci, da kuma ƙafar murabba’i miliyan 750 na iskar gas a kullum domin masana’antun cikin gida, ciki har da DFL FZE da Matatar Dangote.
Ya ce ana sa ran waɗannan yarjejeniyoyi za su jawo zuba jarin da ya haura dala biliyan 20, yayin da ake ci gaba da tattaunawa kan wasu ƙarin yarjejeniyoyi guda bakwai.
Dangane da inganta tsarin gudanar da kamfani, Ojulari ya ce NNPC Ltd ta koma biyan kuɗaɗen shiga Asusun Tarayya a kowane wata tun daga watan Yulin 2025. Haka kuma ta dawo da tsarin fitar da rahoton ayyukan kasuwanci na wata-wata, tare da gudanar da taron farko na bayyana sakamakon kuɗaɗen shiga ga masu zuba jari a watan Nuwamban 2025 domin ƙarfafa gaskiya, riƙon amana da amincewar masu zuba jari.
Ya buƙaci masu ruwa da tsaki a fannin makamashi su wuce matakin hulɗar kasuwanci kawai, su rungumi haɗin gwiwar dabaru wanda zai samar da cikakkiyar sarkar ƙima da kuma gina tattalin arzikin masana’antu mai gasa.
“NNPC Limited ba ta ɗauki kanta a matsayin kamfanin samar da makamashi kawai ba. Muna ganin kanmu a matsayin masu gina tsarin haɗin gwiwa da ke haɗa jarin kuɗi, fasaha, manufofi, ƙwararru da kasuwanni domin samar da ɗorewar alheri ga Najeriya da Afirka baki ɗaya,” in ji shi.
Ojulari ya bayyana cewa harkar makamashi na daga cikin fannoni mafi haɗin kai a duniya, yana mai jaddada cewa babu wata hukuma ko kamfani guda da zai iya buɗe cikakkiyar damar makamashin Afirka shi kaɗai.
Ya ce rashin cikakken haɗin gwiwa tsakanin gwamnatoci, masu zuba jari, kamfanonin mai, masu tsara dokoki da sauran masu ruwa da tsaki na daga cikin manyan ƙalubalen da ke hana Afirka cin moriyar albarkatun man fetur, iskar gas da makamashi mai sabuntawa da take da su.
A cewarsa, duk da cewa Afirka na da kusan kaso 17 cikin 100 na arzikin iskar gas na duniya, har yanzu nahiyar na samun ƙaramin kaso ne kawai na jarin makamashi da ake zubawa a duniya.
Saboda haka ya yi kira ga gwamnatoci, kamfanonin mai na ƙasa, masu zuba jari, hukumomin tsara dokoki, cibiyoyin kuɗi, jami’o’i da kamfanonin samar da ayyuka su haɗa ƙarfi domin mayar da Afirka cibiyar duniya ta zuba jari, fasahar makamashi da samar da ƙima.
Ya ce, “Makomar makamashin Afirka ba za ta dogara kawai da albarkatun da ke ƙarƙashin ƙasarta ba, za ta dogara ne da irin ingancin haɗin gwiwar da za mu gina a tsakaninmu. Damar da ke gabanmu babba ce ƙwarai. Alhakin yana kanmu. Kuma lokaci ya yi da za mu ɗauki mataki.”
Yanzu haka a cika shekaru 25 da ƙaddamar da shi, taron NOG Energy Week ya ci gaba da kasancewa mafi girman taron baje koli da tattaunawa kan harkokin mai, iskar gas da makamashi a nahiyar Afirka, inda yake haɗa shugabannin masana’antar makamashi, masu tsara manufofi, masu zuba jari da masu ƙirƙire-ƙirƙire domin tattauna makomar makamashi, dorewar ci gaba da bunƙasar masana’antu a Najeriya da ma nahiyar Afirka baki ɗaya.





















