Tseren neman kujerar Majalisar Wakilai na Mazaɓar Tarayya ta Chanchaga ya ɗauki sabon salo bayan bayyana takaran Shehu Isah-Usman Dantata, wanda ke takara a ƙarƙashin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC).
Dantata ya yi alƙawarin sanya buƙatun mutanen mazabarsa a gaba idan aka zaɓe shi, tare da mai da hankali kan magance rashin tsaro ta hanyar ƙarfafa mata da matasa da kuma samar da ayyukan yi.
Da yake zantawa da manema labarai a sakatariyar ƙasa ta jam’iyyar da ke Abuja, Hon. Usman Dantata ya kuma yi kira ga matasa da su guji shan miyagun ƙwayoyi da ta’addanci na siyasa, yana gargaɗin su kan ‘yan siyasa waɗanda ake amfani da su a lokacin zaɓe kawai sai su watsar da su bayan haka.
“Zan yi amfani da ofishina wajen ƙarfafa jama’a da taimaka musu wajen samar da ayyukan yi. Ina tabbatar muku cewa zan yi haɗin gwiwa da hukumomin tsaro da shugabannin al’umma har sai an kawar da rashin tsaro gaba ɗaya, In Sha Allah,” inji Usman Dantata.





















