Daga Bashir Bello, Abuja
Kungiyar Matasa ta Kasa (NYA) ta bukaci a dauki matakan da za su hana jam’iyyar All Progressives Congress (APC) takura jam’iyyun adawa domin ba wa jam’iyyar mai mulki sauki a zaben 2027.
Shugaban Matasa na NYA, Jakada Aliyu Bin Abbas, ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da mai taimaka masa akan Harkokin yada labarai da hulda da Jama’a, Okpani Jacob Onjewu Dickson ya sanya hannu, aka rabawa ’yan jarida a Kaduna ranar Alhamis 2 ga Afrilu, 2026.
“An jawo hankalin Kungiyar Matasa ta Kasa (NYA) kan taron ’yan jarida da za a jagoranta da Mai Girma Alhaji Atiku Abubakar tare da shugabannin adawa da masu ruwa da tsaki a siyasa dangane da abubuwan da suka faru a cikin African Democratic Congress (ADC).
“Duk da muna ganin muhimmancin tattaunawar siyasa dole ne mu bayyana cewa halin da Alummar Najeriya ke ciki ya fi muhimmanci fiye da taron ’yan jarida” in ji sanarwar.
Sanarwar mai taken, “SANARWA NA HUKUMA: KIRA GA JAJIRTATTUN SHUGABANNI MASU MAYAR DA HANKALI GA AL’UMMA” ta nuna cewa Najeriya tana tsaye a gagarumin mataki.
“Miliyoyin ’yan kasa musamman matasa, suna fama da rashin tsaro, wahalar tattalin arziki, da jin an yi watsi da su. A irin wannan lokaci mai muhimmanci, shugabanci dole ne ya wuce magana ya nuna jarumta, sadaukarwa, da gaskiya tare da al’umma.
“Saboda haka muna kalubalantar shugabannin gwamnati da na adawa su wuce taron ’yan jarida su rungumi matakai masu karfi da hadin kai da suka dace da halin da ’yan Najeriya ke ciki. Idan da gaske ana son tsayawa tare da al’umma, to ya bayyana ta hanyar:
Zanga-zangar kasa cikin lumana da za ta ba da murya ga radadi da burin ’yan Najeriya. Kira na hadin gwiwa ga azumi da addu’o’i, neman taimakon Allah da warkar da kasa.
Sadaukarwa ta zahiri da ta kashin kai da za ta karfafa gwiwa da dawo da fata a cikin ’yan kasa.”
NYA ta gargadi cewa duk wani abu da bai kai wannan ba zai iya zama kamar al’ada ta siyasa ba tare da jagoranci na gaskiya ba.
“Abin damuwa ne matuka cewa yayin da ’yan siyasa ke saurin hada kai da sake rarrabawa idan mulki yana hannun, ba a ganin irin wannan gaggawa da hadin kai wajen fuskantar manyan kalubale da ke barazana ga kasa musamman rashin tsaro da kare rayuka.
“Gaskiya dole ne a fada: da dama daga cikin shugabanninmu na siyasa, duka a gwamnati da adawa, sun rasa hanya. Abin da Najeriya ke bukata yanzu shi ne sabon tsari na shugabanni masu jarumta, masu sadaukarwa, da masu kare al’umma sama da bukatun kansu ko na siyasa.
“Tarihi ba zai tuna da maganganu ba, zai tuna da ayyuka, jarumta, da sadaukarwa.
“Matasa na wannan kasa suna kallo. Lokacin daukar mataki ya yi yanzu,” in ji sanarwar.





















