Daga Bashir Bello, Abuja
Dan Majalisar Wakilai mai wakiltar Alkaleri da Kirfi daga Jihar Bauchi Hon. Kabiru Yusuf Alhaji yace Jamiyar APC a shirye take ta karbi mai Girma Gwamnan Jihar Bauchi Sanata Bala Muhammad Kauran Bauchi Zuwa Cikin Jamiyar.
Hon. Kabiru Alhaji yayi wannan furucin ne lokacin da yake ganawa da Yan jaridu a Offishinsa dake majalisar a Abuja.
Dan Majalisar Wanda shine yake wakiltar mazabar Gwamnan a majalisar Wakilai yace Duba da irin hazaka da kwazo na Gwamnan duk da cewa Dan Jamiyar PDP ne, babu shakka Idan Kauran Bauchi ya hada Kai da Shugaban Kasa shigowarsa APC zai Kara Bunkasa Jamiyar a Jihar.
Acewar sa Shugaban jamiyar APC na Kasa da Gwamnan Jihar Kano Sun Kai ziyara Jihar Bauchi domin ganawa da Gwamnan don ganin Ya shigo Jamiyar.
Yana mai cewa Shiyasa Jamiyar adawa ta ADC ma take Neman ya shigo inuwarta inda Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya Babachir Lawal shima ya jagoranci Yan tawagar ADC domin zawarcin Gwamna Bala Muhammad.
Harila yau Dan Majalisar ya tabbatar da cewa Jamiyar APC a Jihar Bauchi kanta a hade yake kuma a shirye Suke su tunkari zaben 2027 mai Zuwa Idan Allah ya kaimu.
Bugu da Kari, shima Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima yayi Kira agareshi da ya shigo Jamiyar APC. Ya Kara da cewa kakakin Majalisar Wakilai Dr. Tajudeen Abbas da sauran jigajigan Yan Jamiyar APC suma sun ziyarci Gwamnan Jihar Bauchi.
Daga bisani Dan Majalisar yayi Kira GA Alummar mazabarsa dana Jihar da su cigaba da basu goyon Baya domin Samun Nasara.





















