Daga Bashir Bello, Abuja
Alhaji Kabiru Sani Giant, tsohon Mai Bai wa Gwamnan Jihar Kebbi Shawara kan Harkokin Wutar Lantarki da Siyasa, ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar kujerar Sanata na Kebbi ta tsakiya (Kebbi Central) a karkashin jam’iyyar All Progressives Congress (APC). Wannan sanarwa tasa ta bude fagen fafatawa da Sanata mai ci, Adamu Aliero.
A cikin hirar da aka yi da shi ta WhatsApp, Kabiru ya jaddada cewa duk da kasancewarsa cikin harkokin siyasa tsawon shekaru, yawanci aikinsa ya kasance na tallafawa wasu su samu mukamai. Amma a wannan karon, ya ce shi kansa zai tsaya takara domin “ceto Alummar Kebbi ta tsakiya (Kebbi Central).”
Burinsa shi ne kawo karshen abin da ya kira dogon mulkin siyasa na Sanata Aliero, idan ya samu nasara a zaben fidda gwani na APC. Ya roki al’ummar Kebbi Central da su rungumi sauyi ta hanyar kuri’a, inda ya jaddada bukatar sabuwar kuzari a wakilcin majalisar dattijai.
“Lokaci ya yi da za a mika sandar shugabanci, a dawo da ayyukan majalisa ga matasa masu kuzari a Jihar Kebbi,” in ji shi.
Shigowarsa cikin takarar ya kara tayar da jijiyoyin wuya a siyasar Kebbi, yayin da APC ke shirin fuskantar zaben fidda gwani mai zafi, wanda tsofaffin ‘yan siyasa da sabbin masu neman mukamai ke fafatawa a cikinsa.




















