• Gida
  • Game da Mu
  • Tuntuɓar
  • Advertise
  • Privacy & Policy
Kasuwancin Duniya
Advertisement
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
No Result
View All Result
Kasuwancin Duniya
No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
  • Al’adu da Fasaha
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
Home Uncategorized

Yan Sandan Kaduna Sun Hallaka ‘Yan Garkuwa da Mutane, Sun Kwato Kayan Hasken Rana da Aka Sace na Naira Miliyan 78 da Shanu 410 Cikin Mako Biyu

August 4, 2026
in Uncategorized
Reading Time: 3 mins read
0
Yan Sandan Kaduna Sun Hallaka ‘Yan Garkuwa da Mutane, Sun Kwato Kayan Hasken Rana da Aka Sace na Naira Miliyan 78 da Shanu 410 Cikin Mako Biyu
0
SHARES
6
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsApp

Daga Bashir Bello, Abuja.

Karanta HakananPosts

Dangote, Kamfanin Mai Na Ƙasar Congo Sun Fara Tattaunawa Kan Haɗin Gwiwa a Fannin Tace Mai da Samar da Kayayyakin Man Fetur…

Kamfanin NNPC Ta Sanya Hannu Kan Yarjejeniya Don Fara Aiki da Faɗaɗa Masana’antar Mai ta Warri da Port Harcourt

An Buɗe Kasuwar Baje-Koli ta Duniya karo na 47 a Kaduna; shuwagabannin gwamnati, masana’antu, da na kasuwanci sun yi kira da a fassara sauye-sauyen tattalin arziki da ake yi a Najeriya zuwa ga samun nasarori na zahiri

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kaduna ta samu manyan nasarori cikin makonni biyu da suka gabata, inda ta kama mutane 16 da ake zargi da garkuwa da mutane, ta hallaka wasu fitattun ‘yan bindiga, tare da kwato kadarorin da aka sace na daruruwan miliyoyin naira a sassa daban-daban na jihar.

Da yake jawabi ga manema labarai a wani taron manema labarai da aka gudanar a ranar Litinin, 4 ga Agustan 2026, Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar, CP Rabiu Muhammad, psc, mni, ya bayyana cewa wadannan nasarori sun samu ne sakamakon ci gaba da gudanar da ayyukan tsaro domin tarwatsa kungiyoyin masu aikata laifuka da ke barazana ga zaman lafiya a jihar Kaduna.

CP Rabiu Muhammad ya bayyana cewa a cikin wannan lokaci, jami’an rundunar sun kwato bindigogi guda 10 na nau’o’i daban-daban, inverter na hasken rana guda 190 da darajarsu ta kai Naira miliyan 69, batirin lithium guda 10 da darajarsu ta kai Naira miliyan 9, shanu 410, wayoyin hannu 32 da aka sace, talabijin na plasma guda biyu, mota guda daya da aka sace, da kuma kunshi 83 na haramtattun kwayoyi.

Ya bayyana wasu muhimman nasarori, ciki har da kama Aisha Barau mai shekaru 20 daga kauyen Ramin Kura a ranar 21 ga Yuli, dauke da takardun dalar Amurka na bogi.

Bayan amsa laifin, jami’ai sun kama Abdullahi Muhammad mai shekaru 55 da Danbala Jibrin mai shekaru 57, wadanda ake zargin su ne suka samar mata da kudin bogin.

A ranar 25 ga Yuli kuma, Sashen Yaki da Garkuwa da Mutane ya kama wasu mutane uku da ake zargi da safarar makamai, Luka Samuel mai shekaru 38, John Paul mai shekaru 37 da Musa Elisha mai shekaru 28 a Jos, Jihar Filato.

An kwato bindigogi biyu kirar gida daga hannunsu, kuma sun amsa cewa suna kai wa ‘yan bindiga makamai.

A wani samame da aka kai ranar 24 ga Yuli a kauyen Kargi, hadin gwiwar jami’an ‘yan sanda da kungiyar ‘Yan Sa Kai ta yi sanadin kama Abdullahi Mohammed wanda aka fi sani da “Aala”, mai shekaru 34, wanda ake zargin jagora ne wajen garkuwa da mutane a yankin Kuzuntu da ke Karamar Hukumar Ikara.

Ya amsa cewa yanada hannu a kashe mambobi biyu na ‘Yan Sa Kai a bara. An kwato bindiga kirar AK-47 guda daya da harsasai guda biyar.

Har ila yau, rundunar ta kwato wata mota kirar Toyota Sienna da aka sace daga wani masallaci a Unguwan Rimi bayan kama Mohammed Shehu a Zariya.

Bayan amsa laifinsa ne aka kama Zakari Abubakar, wanda ake zargin kwararre ne wajen kera kwafin makullan motoci.

A ranar 26 ga Yuli, jami’an ‘yan sanda a Zariya sun dakile wani yunkurin satar shanu a kauyen Damanko, inda suka kwato shanu 80 da tumaki 10 bayan musayar wuta da masu laifin.

Mutane biyu da suka samu raunuka sakamakon harin suna ci gaba da karbar magani.

A ranar 28 ga Yuli kuma, jami’an rundunar sun gano wani ma’ajiya a Zariya dauke da kayan aikin hasken rana da aka sace, wadanda darajarsu ta kai Naira miliyan 78. Ana zargin cewa an karkatar da kayan ne yayin da ake jigilar su.

A karshe, a ranar 31 ga Yuli, an kama Alex Odoh mai shekaru 36 da Daniel Eze mai shekaru 35 a Kasuwar Magani bisa zargin samar wa ‘yan bindiga haramtattun kwayoyi.

CP Rabiu Muhammad ya yabawa jami’an rundunar bisa jarumtaka da kwarewar da suka nuna wajen gudanar da ayyukansu.

Ya sake jaddada kudirin rundunar na ci gaba da bin masu aikata laifuka ba tare da sassauci ba, tare da rokon al’umma su rika bai wa jami’an tsaro sahihan bayanan sirri a kan lokaci.

Ya ce, “Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kaduna na aiki tukuru domin tabbatar da cewa jihar ta kasance cikin aminci ga daukacin al’umma. Muna aiki tare da rundunar soji, Hukumar DSS, NSCDC, kungiyoyin ‘yan sa kai da sauran hukumomin tsaro domin cimma wannan buri.”

Ya kuma tabbatar da cewa za a gurfanar da dukkan wadanda ake zargi a gaban kotu bayan kammala bincike.

Previous Post

Tawagar Gwamnatin Kano ta kai ziyarar ta’aziyya ga Sarkin Musulmi kan rasuwar Sardaunan Sakkwato

Next Post

Gwamna Yusuf Ya Tabbatar da Aiwatar da Bin Dokokin Zirga-zirga a Kano

Related Posts

Uncategorized

Dangote, Kamfanin Mai Na Ƙasar Congo Sun Fara Tattaunawa Kan Haɗin Gwiwa a Fannin Tace Mai da Samar da Kayayyakin Man Fetur…

July 1, 2026
Uncategorized

Kamfanin NNPC Ta Sanya Hannu Kan Yarjejeniya Don Fara Aiki da Faɗaɗa Masana’antar Mai ta Warri da Port Harcourt

May 4, 2026
An Buɗe Kasuwar Baje-Koli ta Duniya karo na 47 a Kaduna; shuwagabannin gwamnati, masana’antu, da na kasuwanci sun yi kira da a fassara sauye-sauyen tattalin arziki da ake yi a Najeriya zuwa ga samun nasarori na zahiri
Kasuwanci

An Buɗe Kasuwar Baje-Koli ta Duniya karo na 47 a Kaduna; shuwagabannin gwamnati, masana’antu, da na kasuwanci sun yi kira da a fassara sauye-sauyen tattalin arziki da ake yi a Najeriya zuwa ga samun nasarori na zahiri

February 8, 2026
Saƙon Gaisuwa daga  Kasuwanduniya.com
Uncategorized

Saƙon Gaisuwa daga Kasuwanduniya.com

December 25, 2025
Photo News
Hotuna masu ban Sha’awa

Photo News

November 30, 2025
Next Post
Gwamna Yusuf Ya Tabbatar da Aiwatar da Bin Dokokin Zirga-zirga a Kano

Gwamna Yusuf Ya Tabbatar da Aiwatar da Bin Dokokin Zirga-zirga a Kano

Gwamna Radda Ya Rantsar da Sabbin Sakatarorin Dindindin Hudu

Gwamna Radda Ya Rantsar da Sabbin Sakatarorin Dindindin Hudu

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Trending
  • Comments
  • Latest
“Sayen Wayoyin Hannu Na Zuwa Da Mummunar Matsala” — Abubakar Ubale

“Sayen Wayoyin Hannu Na Zuwa Da Mummunar Matsala” — Abubakar Ubale

January 18, 2026
TARON OPEN MIC WITH SHINE YAFARA YUNKURIN FARFAƊO DA ƊABI’U: MASU JAWABI SUN YABI HANGEN NESAN MR. SHINE

TARON OPEN MIC WITH SHINE YAFARA YUNKURIN FARFAƊO DA ƊABI’U: MASU JAWABI SUN YABI HANGEN NESAN MR. SHINE

June 20, 2026
BA Zamu Sake Yarda ayi Watsi da Matasa Bayan Zabe ba Inji Kungiyar NYA

BA Zamu Sake Yarda ayi Watsi da Matasa Bayan Zabe ba Inji Kungiyar NYA

January 28, 2026
ADC ta samu babban jigo na siyasa Farfesa Sani Bello don aikin duba kundin tsarin mulki bayan Awanni 24 da barin APC

ADC Ta Nuna Sabuwar Zamanin Gaskiya da Aminci ta Hanyar Nada Farfesa Mohammed Sani Bell

January 8, 2026
Sanata Anthony Yaro Ya Gamsu Da Dokar Cin Zarafin yara

Sanata Anthony Yaro Ya Gamsu Da Dokar Cin Zarafin yara

0
Zamu Fara Bincike A Kan Matuka Jiragen Sama Don Hanasu Shan Kayan Maye, Inji Sanata Buhari Abdulfatah

Zamu Fara Bincike A Kan Matuka Jiragen Sama Don Hanasu Shan Kayan Maye, Inji Sanata Buhari Abdulfatah

0
Kudirin Dokar Cibiyar Hukumar EFCC Ta Tsallake karatu Na Biyu

Kudirin Dokar Cibiyar Hukumar EFCC Ta Tsallake karatu Na Biyu

0
Yan Majalisa da Ma’aikatar Yan Sanda sun goyi bayan kashi 15% na Mata Wurin daukar aiki

Yan Majalisa da Ma’aikatar Yan Sanda sun goyi bayan kashi 15% na Mata Wurin daukar aiki

0
Mauludi: Sabunta Alkawarinmu ga Zaman Lafiya, Tausayi da Jinƙai

Mauludi: Sabunta Alkawarinmu ga Zaman Lafiya, Tausayi da Jinƙai

August 26, 2026
Mauludi: Ku yi addu’ar farfaɗowar tattalin arziki da inganta tsaro — Ashiru ya roƙi al’ummar Musulmi

Mauludi: Ku yi addu’ar farfaɗowar tattalin arziki da inganta tsaro — Ashiru ya roƙi al’ummar Musulmi

August 25, 2026
Aikin Bonga Kudu-Maso-Yamma Aparo: NNPC, Ƙungiyoyin Maƙasanta na OML 118 Sun Kulla Ƙarin Yarjejeniyar PSC da DSA

Aikin Bonga Kudu-Maso-Yamma Aparo: NNPC, Ƙungiyoyin Maƙasanta na OML 118 Sun Kulla Ƙarin Yarjejeniyar PSC da DSA

August 24, 2026
Kamfanin Dangote Cement ta yi bikin Ranar Matasa a Obajana tare da sabunta kudirin ci gaban matasa.

Kamfanin Dangote Cement ta yi bikin Ranar Matasa a Obajana tare da sabunta kudirin ci gaban matasa.

August 19, 2026

Recent News

Mauludi: Sabunta Alkawarinmu ga Zaman Lafiya, Tausayi da Jinƙai

Mauludi: Sabunta Alkawarinmu ga Zaman Lafiya, Tausayi da Jinƙai

August 26, 2026
Mauludi: Ku yi addu’ar farfaɗowar tattalin arziki da inganta tsaro — Ashiru ya roƙi al’ummar Musulmi

Mauludi: Ku yi addu’ar farfaɗowar tattalin arziki da inganta tsaro — Ashiru ya roƙi al’ummar Musulmi

August 25, 2026
Aikin Bonga Kudu-Maso-Yamma Aparo: NNPC, Ƙungiyoyin Maƙasanta na OML 118 Sun Kulla Ƙarin Yarjejeniyar PSC da DSA

Aikin Bonga Kudu-Maso-Yamma Aparo: NNPC, Ƙungiyoyin Maƙasanta na OML 118 Sun Kulla Ƙarin Yarjejeniyar PSC da DSA

August 24, 2026
Kamfanin Dangote Cement ta yi bikin Ranar Matasa a Obajana tare da sabunta kudirin ci gaban matasa.

Kamfanin Dangote Cement ta yi bikin Ranar Matasa a Obajana tare da sabunta kudirin ci gaban matasa.

August 19, 2026
Kasuwancin Duniya

© 2025 Kasuwancin Duniya - Wanda ya tsara AuspiceWeb.

Kewaya Site

  • Gida
  • Game da Mu
  • Tuntuɓar
  • Advertise
  • Privacy & Policy

Biyo Mu

No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni

© 2025 Kasuwancin Duniya - Wanda ya tsara AuspiceWeb.

Powered by
►
Necessary cookies enable essential site features like secure log-ins and consent preference adjustments. They do not store personal data.
None
►
Functional cookies support features like content sharing on social media, collecting feedback, and enabling third-party tools.
None
►
Analytical cookies track visitor interactions, providing insights on metrics like visitor count, bounce rate, and traffic sources.
None
►
Advertisement cookies deliver personalized ads based on your previous visits and analyze the effectiveness of ad campaigns.
None
►
Unclassified cookies are cookies that we are in the process of classifying, together with the providers of individual cookies.
None
Powered by