• Gida
  • Game da Mu
  • Tuntuɓar
  • Advertise
  • Privacy & Policy
Kasuwancin Duniya
Advertisement
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
No Result
View All Result
Kasuwancin Duniya
No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
  • Al’adu da Fasaha
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
Home Labarai

Gwamna Radda Ya Rantsar da Sabbin Sakatarorin Dindindin Hudu

Ya Bukaci Manyan Ma'aikata Su Zama Jagorori ga Sabbin Ma'aikatan Gwamnati

August 5, 2026
in Labarai
Reading Time: 4 mins read
0
Gwamna Radda Ya Rantsar da Sabbin Sakatarorin Dindindin Hudu
0
SHARES
7
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsApp

Ya Ce Kowace Karamar Hukuma Ta Cancanci Samun Damar Samar da Manyan Ma’aikatan Gwamnati

Karanta HakananPosts

Mauludi: Sabunta Alkawarinmu ga Zaman Lafiya, Tausayi da Jinƙai

Mauludi: Ku yi addu’ar farfaɗowar tattalin arziki da inganta tsaro — Ashiru ya roƙi al’ummar Musulmi

RUNDUNAR ‘YAN SANDA KADUNA TA AMSA BIDION DA YA YADU, TA GARGADI JAMI’AI KAN CIN HANCIN DA HALAYEN DA BA DAI DAI BA

Daga Bashir Bello, Abuja

The to theGwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya rantsar da sabbin Sakatarorin Dindindin guda hudu a ranar Laraba, inda ya sake jaddada kudirin gwamnatinsa na gina ma’aikatar gwamnati mai kwarewa, inganci da kuma tsarin daukaka ma’aikata bisa cancanta.

Sabbin Sakatarorin Dindindin din sun hada da Malam Abdu Usman, Dakta Sani Suleiman, Dakta Shamsuddeen Yahaya Suleiman da Dakta Hussaini Hamisu Yanduna.

Da yake jawabi jim kadan bayan rantsar da su a Fadar Gwamnatin Jihar Katsina, Gwamna Radda ya ce nadin ya nuna kudirin gwamnatinsa na ba wa masu kwarewa, jajircewa da nagarta lada, maimakon la’akari da alaka ta kashin kai.

Ya ce, “An gudanar da dukkan tsarin zaben ne bisa ka’idojin aikin gwamnati da aka tanada. Wadanda aka rantsar a yau sun samu mukamansu ne saboda cancanta, kwarewa, jajircewa da sadaukar da kai wajen aiki.”

Gwamna Radda ya taya sabbin Sakatarorin Dindindin murna, tare da yin kira gare su da su tabbatar sun cika amanar da aka dora musu ta hanyar gaskiya, rikon amana, kwarewa da kuma sadaukar da kai wajen yi wa al’ummar Jihar Katsina hidima.

Ya jaddada cewa rantsuwar aiki da suka yi ta kasance abin tunatarwa a kodayaushe game da nauyin da ke kansu ga gwamnati da al’ummar jihar.

Ya ce, “Rantsuwar aiki ba wani biki kawai ba ne. Alkawari ne na gaskiya, rikon amana da kuma yi wa jama’a hidima cikin aminci. Idan kuka yi aiki bisa wadannan ka’idoji, za ku yi nasara kuma ku bar abin koyi ga masu zuwa bayanku.”
Gwamnan ya kuma bayyana cewa an zabo sabbin Sakatarorin Dindindin din ne daga kananan hukumomi daban-daban na jihar, yana mai cewa hakan wani bangare ne na kokarin tabbatar da adalci da bai wa kowa dama a ma’aikatar gwamnatin jihar.

Sai dai ya nuna damuwarsa cewa akwai wasu kananan hukumomi da ba su samu damar samar da wadanda suka cancanta ba, saboda rashin jami’an da suka kai matakin mukami da ake bukata ko kuma wadanda ke da cancantar shiga tsarin tantancewar.

Ya ce, “Muna fatan kuma muna addu’ar cewa nan gaba kowace Karamar Hukuma a Jihar Katsina za ta samar da kwararrun jami’ai masu cancantar fafatawa da kuma zama Sakatarorin Dindindin.”

Yana sake jaddada manufofin gwamnatinsa na gyaran ma’aikatar gwamnati, Gwamna Radda ya ce ya zama wajibi a bai wa kowane ma’aikaci dama ta ci gaba bisa cancanta da irin aikin da yake yi.
Ya ce, “Burinmu shi ne gina ma’aikatar gwamnati inda kowa zai samu damar daukaka bisa cancanta, ba wai saboda wanda ya sani ba, ko inda ya fito, ko kuma dangantakar iyali. Cancanta, kwarewa, gaskiya da jajircewa su ne za su kasance a gaba a ko da yaushe.”

Gwamnan ya umurci sabbin Sakatarorin Dindindin da su tabbatar da adalci, gaskiya da bin ka’ida a Ma’aikatunsu, Hukumominsu da Cibiyoyinsu, musamman wajen daukar ma’aikata, karin girma da ci gaban sana’a.

Haka kuma ya bukaci Daraktoci da sauran manyan ma’aikatan gwamnati su dauki nauyin koyarwa da jagorantar matasa ma’aikata ta hanyar ba su shawarwari, mika ilimi da kuma kara musu kwarewa.

Ya ce, “Ina kira ga manyan ma’aikatan gwamnati da su ci gaba da jagorantar matasa ma’aikata tare da inganta kwarewarsu. Ta wannan hanyar ne za mu dore da sauye-sauyen da muke aiwatarwa tare da tabbatar da ci gaba mai dorewa a ma’aikatar gwamnati.”

Gwamna Radda ya bayyana kwarin gwiwarsa cewa sabbin Sakatarorin Dindindin za su kara karfafa sauye-sauyen da ake yi a ma’aikatar gwamnatin jihar tare
da inganta ayyukan gwamnati ga al’umma.

Ya kuma ce gwamnatinsa za ta ci gaba da karfafa cibiyoyin gwamnati, bunkasa kwarewa da kuma fadada amfani da fasahar zamani a Ma’aikatu, Hukumomi da Cibiyoyi domin ma’aikatar gwamnati ta fi biyan bukatun al’umma.

Sabbin Sakatarorin Dindindin da aka rantsar kwararru ne a fannoni daban-daban:
Malam Abdu Usman yana da Digiri na Biyu (Master’s Degree) a fannin Manufofin Jama’a da Gudanar da Mulki (Public Policy and Administration), kuma yana da fiye da shekaru talatin yana aiki a Ma’aikatar Gwamnatin Jihar Katsina.

Ya yi aiki a KSACDP/IFAD, KTARDA, Fadar Gwamnati, KATSACA, kwamitocin gwamnati da kuma Ofishin Sakataren Gwamnatin Jihar.

Dakta Sani Suleiman ya samu digirin MBBS daga Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, sannan kuma Fellow ne na West African College of Physicians. Ya yi aiki a Asibitin Koyarwa na ABUTH, manyan asibitocin jihar Katsina, Ma’aikatar Lafiya da Hukumar Gudanar da Ayyukan Asibitoci.

Dakta Shamsuddeen Yahaya Suleiman yana da digirin MBBS daga Jami’ar Ahmadu Bello, Digiri na Biyu (Master’s Degree) a fannin Tattalin Arzikin Lafiya (Health Economics) daga Jami’ar Bayero Kano, sannan yana da Digirin Digirgir (Ph.D.) a fannin Kiwon Lafiyar Jama’a.

Ya taba zama Babban Sakataren Hukumar Kula da Lafiya ta Farko ta Jihar Katsina, inda ya jagoranci sauye-sauye domin inganta ayyukan kiwon lafiya na matakin farko.

Dakta Hussaini Hamisu Yanduna yana da takardun kwarewa a fannonin Lafiyar Hakora, Lafiyar Al’umma da Kiwon Lafiyar Jama’a, ciki har da Digiri na Biyu (Master’s Degree) a Kiwon Lafiyar Jama’a. Ya yi aiki a manyan asibitoci da Hukumar Gudanar da Lafiya ta Farko.

Haka kuma ya taba zama Shugaban Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC), Reshen Jihar Katsina, da kuma Kungiyar Hadin Gwiwar Ma’aikatan Bangaren Lafiya.

Previous Post

Gwamna Yusuf Ya Tabbatar da Aiwatar da Bin Dokokin Zirga-zirga a Kano

Next Post

Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da Sauyi a Ilimin Almajiranci ta Kuma haramta bara a titi

Related Posts

Mauludi: Sabunta Alkawarinmu ga Zaman Lafiya, Tausayi da Jinƙai
Labarai

Mauludi: Sabunta Alkawarinmu ga Zaman Lafiya, Tausayi da Jinƙai

August 26, 2026
Mauludi: Ku yi addu’ar farfaɗowar tattalin arziki da inganta tsaro — Ashiru ya roƙi al’ummar Musulmi
Labarai

Mauludi: Ku yi addu’ar farfaɗowar tattalin arziki da inganta tsaro — Ashiru ya roƙi al’ummar Musulmi

August 25, 2026
RUNDUNAR YAN SANDAR JIHAR KADUNA SUN YI ALLAH WADAI DA KISAN GILLA DA AKAYI MA WASU MATAFIYA, SUN KAMA MUTUM 6 KAN KASHE MUTUM 2 MARASA LAIFI
Labarai

RUNDUNAR ‘YAN SANDA KADUNA TA AMSA BIDION DA YA YADU, TA GARGADI JAMI’AI KAN CIN HANCIN DA HALAYEN DA BA DAI DAI BA

August 18, 2026
Gwamna Yusuf Ya Tabbatar da Aiwatar da Bin Dokokin Zirga-zirga a Kano
Labarai

Gwamna Yusuf Ya Tabbatar da Aiwatar da Bin Dokokin Zirga-zirga a Kano

August 4, 2026
Tawagar Gwamnatin Kano ta kai ziyarar ta’aziyya ga Sarkin Musulmi kan rasuwar Sardaunan Sakkwato
Labarai

Tawagar Gwamnatin Kano ta kai ziyarar ta’aziyya ga Sarkin Musulmi kan rasuwar Sardaunan Sakkwato

August 4, 2026
Ɗan Takara na Shugaban Ƙasa na ADC Atiku Abubakar Ya Yi Ta’aziyya Ga Masarautar Bungudu Kan Harin da Aka Kai.
Labarai

Ɗan Takara na Shugaban Ƙasa na ADC Atiku Abubakar Ya Yi Ta’aziyya Ga Masarautar Bungudu Kan Harin da Aka Kai.

August 3, 2026
Next Post
Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da Sauyi a Ilimin Almajiranci ta Kuma haramta bara a titi

Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da Sauyi a Ilimin Almajiranci ta Kuma haramta bara a titi

NNPC TAYI NASARAN SAMAR DA DANYEN MAI ZUWA GANGA MILIYAN 1.67 A RANA, TA KARYATA ZARGIN GAZAWA A ZANGON RABA LASISIN HAKAR MAI

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Trending
  • Comments
  • Latest
“Sayen Wayoyin Hannu Na Zuwa Da Mummunar Matsala” — Abubakar Ubale

“Sayen Wayoyin Hannu Na Zuwa Da Mummunar Matsala” — Abubakar Ubale

January 18, 2026
TARON OPEN MIC WITH SHINE YAFARA YUNKURIN FARFAƊO DA ƊABI’U: MASU JAWABI SUN YABI HANGEN NESAN MR. SHINE

TARON OPEN MIC WITH SHINE YAFARA YUNKURIN FARFAƊO DA ƊABI’U: MASU JAWABI SUN YABI HANGEN NESAN MR. SHINE

June 20, 2026
BA Zamu Sake Yarda ayi Watsi da Matasa Bayan Zabe ba Inji Kungiyar NYA

BA Zamu Sake Yarda ayi Watsi da Matasa Bayan Zabe ba Inji Kungiyar NYA

January 28, 2026
ADC ta samu babban jigo na siyasa Farfesa Sani Bello don aikin duba kundin tsarin mulki bayan Awanni 24 da barin APC

ADC Ta Nuna Sabuwar Zamanin Gaskiya da Aminci ta Hanyar Nada Farfesa Mohammed Sani Bell

January 8, 2026
Sanata Anthony Yaro Ya Gamsu Da Dokar Cin Zarafin yara

Sanata Anthony Yaro Ya Gamsu Da Dokar Cin Zarafin yara

0
Zamu Fara Bincike A Kan Matuka Jiragen Sama Don Hanasu Shan Kayan Maye, Inji Sanata Buhari Abdulfatah

Zamu Fara Bincike A Kan Matuka Jiragen Sama Don Hanasu Shan Kayan Maye, Inji Sanata Buhari Abdulfatah

0
Kudirin Dokar Cibiyar Hukumar EFCC Ta Tsallake karatu Na Biyu

Kudirin Dokar Cibiyar Hukumar EFCC Ta Tsallake karatu Na Biyu

0
Yan Majalisa da Ma’aikatar Yan Sanda sun goyi bayan kashi 15% na Mata Wurin daukar aiki

Yan Majalisa da Ma’aikatar Yan Sanda sun goyi bayan kashi 15% na Mata Wurin daukar aiki

0
Mauludi: Sabunta Alkawarinmu ga Zaman Lafiya, Tausayi da Jinƙai

Mauludi: Sabunta Alkawarinmu ga Zaman Lafiya, Tausayi da Jinƙai

August 26, 2026
Mauludi: Ku yi addu’ar farfaɗowar tattalin arziki da inganta tsaro — Ashiru ya roƙi al’ummar Musulmi

Mauludi: Ku yi addu’ar farfaɗowar tattalin arziki da inganta tsaro — Ashiru ya roƙi al’ummar Musulmi

August 25, 2026
Aikin Bonga Kudu-Maso-Yamma Aparo: NNPC, Ƙungiyoyin Maƙasanta na OML 118 Sun Kulla Ƙarin Yarjejeniyar PSC da DSA

Aikin Bonga Kudu-Maso-Yamma Aparo: NNPC, Ƙungiyoyin Maƙasanta na OML 118 Sun Kulla Ƙarin Yarjejeniyar PSC da DSA

August 24, 2026
Kamfanin Dangote Cement ta yi bikin Ranar Matasa a Obajana tare da sabunta kudirin ci gaban matasa.

Kamfanin Dangote Cement ta yi bikin Ranar Matasa a Obajana tare da sabunta kudirin ci gaban matasa.

August 19, 2026

Recent News

Mauludi: Sabunta Alkawarinmu ga Zaman Lafiya, Tausayi da Jinƙai

Mauludi: Sabunta Alkawarinmu ga Zaman Lafiya, Tausayi da Jinƙai

August 26, 2026
Mauludi: Ku yi addu’ar farfaɗowar tattalin arziki da inganta tsaro — Ashiru ya roƙi al’ummar Musulmi

Mauludi: Ku yi addu’ar farfaɗowar tattalin arziki da inganta tsaro — Ashiru ya roƙi al’ummar Musulmi

August 25, 2026
Aikin Bonga Kudu-Maso-Yamma Aparo: NNPC, Ƙungiyoyin Maƙasanta na OML 118 Sun Kulla Ƙarin Yarjejeniyar PSC da DSA

Aikin Bonga Kudu-Maso-Yamma Aparo: NNPC, Ƙungiyoyin Maƙasanta na OML 118 Sun Kulla Ƙarin Yarjejeniyar PSC da DSA

August 24, 2026
Kamfanin Dangote Cement ta yi bikin Ranar Matasa a Obajana tare da sabunta kudirin ci gaban matasa.

Kamfanin Dangote Cement ta yi bikin Ranar Matasa a Obajana tare da sabunta kudirin ci gaban matasa.

August 19, 2026
Kasuwancin Duniya

© 2025 Kasuwancin Duniya - Wanda ya tsara AuspiceWeb.

Kewaya Site

  • Gida
  • Game da Mu
  • Tuntuɓar
  • Advertise
  • Privacy & Policy

Biyo Mu

No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni

© 2025 Kasuwancin Duniya - Wanda ya tsara AuspiceWeb.

Powered by
►
Necessary cookies enable essential site features like secure log-ins and consent preference adjustments. They do not store personal data.
None
►
Functional cookies support features like content sharing on social media, collecting feedback, and enabling third-party tools.
None
►
Analytical cookies track visitor interactions, providing insights on metrics like visitor count, bounce rate, and traffic sources.
None
►
Advertisement cookies deliver personalized ads based on your previous visits and analyze the effectiveness of ad campaigns.
None
►
Unclassified cookies are cookies that we are in the process of classifying, together with the providers of individual cookies.
None
Powered by