Daga Bashir Bello, Abuja.
Hankalin Rundunar Yan Sanda Jihar Kaduna ya karkata kan wani bidiyo da ya yadu a kafafen sada zumunta, inda aka ga wasu jami’an ‘yan sanda suna gudanar da binciken ababen hawa tare da karɓar kuɗi daga direbobi da masu babura.
Kwamishinan ‘Yan Sanda, CP Rabiu Muhammad, psc, mni, ya bayar da umarnin a gano jami’an da abin ya shafa nan take, a gayyace su don cikakken bincike, kuma duk wanda aka samu da laifi za a hukunta shi yadda ya dace.
Hakan Yana kunshe ne a wata Sanarwa dauke da sa hannun
Mai Magana da Yawun ‘Yan Sanda
Koman ‘Yan Sanda Jihar Kaduna DSP Mansir Hassan.
A cewar sanarwan, rundunar yana so ya fayyace cewa an rage yin shingen hanya da binciken ababen hawa, sai dai idan akwai sahihin bayanan sirri kan motsin ‘yan ta’adda, makamai, ko wasu abubuwa da aka haramta.
Sai dai rundunar ya lura cewa hanyar da aka nuna a bidiyon ta taba kasancewa hanyar da ‘yan ta’adda ke amfani da ita, tana cikin unguwar Millennium City. A kan wannan hanya ne jami’an ‘yan sanda suka taba kwato bindigogi AK-47 guda 20. Duk da wadannan matsalolin tsaro, CP ya bayyana a fili cewa babu wani jami’in ‘yan sanda da aka yarda ya yi amfani da aikin tsaro na gaskiya a matsayin hanyar karɓar cin hanci, tsangwama, ko wani irin rashin da’a.
Duk jami’in da aka samu da laifi zai fuskanci tsauraran matakan ladabtarwa da na shari’a.
Kwamishinan ‘Yan Sanda ya yaba wa jama’a bisa wayar da kan su, ya kuma bukace su da su ci gaba da bayar da rahoton duk wani rashin kwarewa daga jami’an ‘yan sanda.
Harila yau sanarwan yace ana iya yin korafi ga Sashen Karɓar Koke na ‘Yan Sanda akan lambar waya kaman haka (CRU) a 09049498983, 08075391105, 07039675856.
Rundunar ya ci gaba da jajircewa wajen gudanar da aikin ‘yan sanda na kwararru, bin doka da oda, da kuma kare ‘yancin jama’a da tsaron dukkan mazauna Jihar Kaduna.




















