Daga Bashir Bello, Abuja
Ɗan takarar gwamnan jihar Kaduna na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), Hon. Isa Ashiru, ya buƙaci al’ummar Musulmi a faɗin jihar Kaduna da Najeriya baki ɗaya da su yi amfani da lokacin bikin Mauludi wajen gudanar da addu’o’i na musamman domin samun farfaɗowar tattalin arziki, inganta tsaro da kuma kyakkyawar makoma ga dukkan ’yan ƙasa.
Ashiru ya bayyana hakan ne a cikin saƙon fatan alheri da ya fitar domin tunawa da ranar haihuwar Annabi Muhammad (SAW), wanda Abdulwaheed Olayinka Adubi, mai magana da yawun Hon. Isa Ashiru (Sarkin Bai Zazzau), ɗan takarar gwamnan Kaduna a ƙarƙashin jam’iyyar ADC, ya sanya wa hannu.
Ya yi kira ga Musulmi da su yi tunani a kan koyarwar Annabi Muhammad (SAW), musamman kan tausayi, adalci, tawali’u, sadaukarwa da zaman lafiya tsakanin al’umma.
Ya kuma buƙaci al’ummar Musulmi da su yi addu’a ga shugabanni a dukkan matakan gwamnati, tare da roƙon Allah Ya kawo ɗauki daga cikin matsalolin tattalin arzikin ƙasar, musamman tashin farashin kayayyaki da tsadar rayuwa da kuma ƙalubalen da iyalai, ma’aikata, manoma, ’yan kasuwa da matasa ke fuskanta.
Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun ɗan takarar gwamnan ADC, Rt. Hon. Isa Ashiru, Abdulwaheed Olayinka Adubi, ya rabawa manema labarai a Kaduna ranar Litinin.
Ashiru ya ce:
“Yayin da muke bikin tunawa da haihuwar Annabi Muhammad (SAW), mu sake sabunta jajircewarmu ga ƙa’idojin zaman lafiya, adalci, tausayi da yi wa bil’adama hidima waɗanda Annabi ya kasance abin koyi a kansu.
“A wannan lokaci mai cike da ƙalubale, ya kamata mu ci gaba da yin addu’a domin farfaɗowar tattalin arziki, inganta tsaro da kuma kawo ƙarshen wahalhalun da miliyoyin ’yan Najeriya ke fuskanta. Haka kuma, ya kamata mu yi addu’a Allah Ya ba shugabanninmu hikimar yanke shawarwarin da za su inganta jin daɗi da martabar al’ummarmu.”
Ashiru ya kuma yi kira da a ci gaba da ƙoƙarin magance matsalar rashin tsaro, yana mai jaddada cewa ba za a iya samun ci gaban tattalin arziki mai ma’ana ba matuƙar ’yan ƙasa ba su da damar rayuwa, aiki da gudanar da sana’o’insu na halal cikin aminci.
Ya roƙi al’ummar Musulmi da su yi amfani da wannan lokaci wajen haɓaka haɗin kai, haƙuri da zaman lafiya, ba tare da la’akari da bambancin siyasa, ƙabila ko addini ba.
Ɗan takarar gwamnan na ADC ya kuma yi kira ga ’yan Najeriya da su kasance masu kyakkyawan fata tare da jajircewa wajen gina al’ummar da gwamnati ke da alhakin yin bayani kan ayyukanta, hukumomi ke gudanar da aikinsu yadda ya kamata, kuma kowane ɗan ƙasa ke da damar samun ci gaba da wadata cikin daidaito.
Ya bayyana kwarin gwiwar cewa, idan aka samu shugabanci nagari, gwamnati mai manufa, tare da addu’o’i da goyon bayan ’yan ƙasa, Najeriya za ta iya shawo kan ƙalubalen da take fuskanta a yanzu, ta koma kan turbar ci gaba mai ɗorewa.
Ashiru ya yi wa al’ummar Musulmi a jihar Kaduna da sauran sassan Najeriya fatan samun bikin Mauludi mai cike da zaman lafiya da albarkar ruhaniya, tare da kira gare su da su ci gaba da riƙe koyarwa da kyawawan halayen Annabi Muhammad (SAW).



















