Ƙungiyar yaƙin neman zaɓen Hon. Yusuf Ibrahim Zailani ta yi Allah wadai da yadda aka gudanar da zaɓen fidda gwanin jam’iyyar All Progressives Congress na Gundumar Sanata ta Kaduna ta Tsakiya, tana mai cewa babu wani zaɓe da ya gudana a dukkanin ƙananan hukumomi bakwai na yankin.
Da yake jawabi a taron manema labarai da aka gudanar a Kaduna, Mataimakin Darakta Janar Dr. Cafra Caino ya ce magoya bayan jam’iyyar sun taru a rumfunan zaɓe na mazabunsu, sun jira sa’o’i da dama ba tare da jami’an zaɓe ko kayan zaɓe sun iso ba. Ya ce tsarin ya yi karo da dukkan matakai da ƙa’idojin da Kwamitin Gudanarwa na Ƙasa na APC ya gindaya, yana mai bayyana shi a matsayin gazawa ga dimokuraɗiyyar cikin gida.
Ƙungiyar ta ce sanarwar sakamakon da aka yi tana haifar da tambayoyi masu girma kan gaskiyar wannan aiki, kuma ba zai iya nuna ra’ayin mambobin APC na yankin ba.
Saboda haka ta ki amincewa da sakamakon, tana mai kira ga Kwamitin gudanarwa na NWC, Kwamitin Zaɓe na Jam’iyyar na Jihar Kaduna, da sauran masu ruwa da tsaki da Suyi abinda ya dace su Rusa rashin gaskiya da rashin Adalci.
Sun kuma tabbatar da cewa muddin Jamiyar Taki yin abinda ya dace to babu shakka zai iya Zama sanadin rashin Nasara a zaben 2027 Idan Allah ya kaimu.
Tinda farko a hirar da yayi da manema labarai Tsohon kakakin Majalisar dokokin Jihar Kaduna kuma har ila yau, Dan Takaran Sanatan Kaduna ta Tsakiya Hon. Yusuf Zailani ya Yabawa Magoya bayansa da Suka fito domin Kada kuria Suka Zauna Cikin Rana da Ruwan sama a sassa na kananan hukumomi 7 dake Kaduna ta Tsakiya Amma jamian Zaben Suka ki Zuwa.
Yana mai Kira agaresu da su kwantar da hankalinsu, su kuma bi doka da oda domin a shirye yake yayi duk Mai yuwa Wajen tabbatar da gaskiya da Adalci.
Wannan lamarin dai Masu sharhi Akan al’amuran yau da kullum sun tabbatar da cewa Idan Jamiyar APC ta kuskura ta Zabi Wanda Jama’a Basu so to ta kama hanyar faduwa a zaben 2027





















