• Gida
  • Game da Mu
  • Tuntuɓar
  • Advertise
  • Privacy & Policy
Kasuwancin Duniya
Advertisement
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
No Result
View All Result
Kasuwancin Duniya
No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
  • Al’adu da Fasaha
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni
Home Siyasa

Kakakin Majalisar Wakilai Abbas Ya Kare Ayyukan Majalisa Ta 10, Ya Ce Buɗaɗɗen Tsari, Gyaran Haraji da Muhimman Dokoki Dasuka Sa Majalisar Ta Kafa Tarihi Mai Kyau

July 26, 2026
in Siyasa
Reading Time: 6 mins read
0
Kakakin Majalisar Wakilai Abbas Ya Kare Ayyukan Majalisa Ta 10, Ya Ce Buɗaɗɗen Tsari, Gyaran Haraji da Muhimman Dokoki Dasuka Sa Majalisar Ta Kafa Tarihi Mai Kyau
0
SHARES
12
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsApp

Daga Bashir Bello, NASS, Abuja

A wannan tattaunawa ta musamman da wasu yan jarida da aka Zaba suka yi da shi, Kakakin Majalisar Wakilai, Rt. Hon. Tajudeen Abbas, ya yi waiwaye kan yadda Majalisar Dokoki ta Ƙasa zango ta 10 ta gudanar da ayyukanta, inda ya bayyana shi amatsayin jajircewarta wajen tabbatar da gaskiya da riƙon amana, gyaran dokoki da kuma haɗa ‘yan ƙasa cikin harkokin majalisa.

Karanta HakananPosts

YANKIN AREWA TA ZABI HANYAR DA TAKESO: ABBAS NA JAMIYAR ADP YA GINA TSARI A KAN KANANAN HUKUMOMI 774 KAFIN 2027

Shugabar Jamiyar LP ta yi kira da a yi zaɓen 2027 cikin lumana

Gwamna Yusuf Ya Sake Jaddada Kudirinsa Na Aiwatar da Tsarin Cigaban Kano

Tambaya
Mai Girma Kakakin Majalisa, wannan ne karo na uku da kuke shirya irin wannan ganawa da ‘yan jarida, ‘Yan Najeriya da dama suna tambayar dalilin da ya sa kuke ci gaba da shirya waɗannan zaman. Mene ne babban manufarsa?

Kakakin Majalisa Abbas
Da farko, ina godiya ga Allah Maɗaukakin Sarki saboda rahamarsa.
Tun bayan da na zama Kakakin Majalisar Wakilai, na ɗauki alƙawarin cewa Majalisar Wakilai za ta gudanar da ayyukanta cikin buɗaɗɗen tsari da kuma gaskiya.

Ɗaya daga cikin darussan da muka koya daga Majalisun da suka gabata shi ne cewa ‘yan Najeriya da dama ba su san abin da Majalisar Dokoki ta Ƙasa ke yi ba saboda ba a isar da bayanan ayyukanmu yadda ya kamata.
Shi ya sa Majalisar Wakilai zango ta 10 ta yanke shawarar buɗe ƙofofinta ga ‘yan Najeriya.
Muna son ‘yan ƙasa ba wai kawai su san abin da muke yi ba, har ma su shiga cikin aikin ta hanyar bayar da shawarwari, gano wuraren da ke buƙatar gyara da kuma taimaka mana wajen ƙarfafa aikinmu na majalisa.

A lokacin Makon Buɗaɗɗen Majalisa (Open Week) da muka gudanar kwanan nan, mun shafe kwanaki da dama muna nazarin ayyukanmu, manufofinmu da nasarorinmu na fannin dokoki.
Mun gayyaci matasa, ƙungiyoyin mata, sarakunan gargajiya, ƙungiyoyin fararen hula da kuma ‘yan ƙasa daga sassa daban-daban na ƙasar nan domin su tattauna kai tsaye da ‘yan majalisa.
Wannan ganawa ta yi nasara kuma ta samar mana da muhimman shawarwari da suka amfanar da Majalisar Wakilai.

Tambaya
Shin kuna tattara shawarwarin da ake bayarwa a irin waɗannan ganawa sannan ku yi amfani da su wajen aikinku na majalisa?

Kakakin Majalisa Abbas
Lallai kuwa.
Manufar ba wai kawai ita ce mu nuna abin da muka yi ba, amma domin bai wa ‘yan Najeriya damar tantance yadda muka gudanar da ayyukanmu.
Muna gabatar da ayyukanmu na fannin dokoki, ayyukan sa ido da kuma hulɗarmu da mazabu, sannan mu gayyaci mutane su yi mana suka mai ma’ana tare da bayar da shawarwari.

Harilayau, Ra’ayoyinsu da abubuwan da suka lura da su suna taimaka mana wajen inganta ayyukanmu tare da tsara abubuwan da za su kasance a sahun gaba na ayyukanmu na majalisa a nan gaba.

Tambaya
Me za ku bayyana a matsayin manyan nasarorin da Majalisar Dokoki ta Ƙasa zango ta 10 ta samu?

Kakakin Majalisa Abbas
Madalla, babu shakka majalisar Wakilai zango ta 10 ta samu gagarumin nasarori a fannin samar da dokoki a tarihin dimokuraɗiyyar Najeriya.
Mun tantance tare da amincewa da ƙudirin dokoki fiye da Majalisun da suka gabata, kuma Shugaba Kasa Bola Ahmed Tinubu ya sanya hannu kan adadi mafi yawa daga cikinsu fiye da yadda aka taɓa samu.
Daya daga cikin manyan nasarorin ita ce Shirin Lamunin Karatu na Ɗalibai (Student Loan Scheme), wanda ya bai wa sama da ɗaliban Najeriya miliyan ɗaya damar samun ilimi mai zurfi ba tare da hana su wannan dama ba saboda matsalolin kuɗi.
Wani muhimmin ci gaba kuma shi ne shirin gyaran haraji (Tax Reform).
Najeriya ba za ta iya ci gaba da dogaro kusan gaba ɗaya kan kuɗaɗen shiga daga man fetur ba.
An tsara gyaran harajin ne domin faɗaɗa kuɗaɗen shiga na gwamnati, inganta harkokin kuɗaɗen gwamnati da kuma ba da damar ƙarin zuba jari a hanyoyi, makarantu, asibitoci da sauran muhimman ababen more rayuwa.
An fara aiwatar da waɗannan gyare-gyare a wannan shekara, kuma muna sa ran tasirinsu na dogon lokaci zai ƙara bayyana a cikin shekaru masu zuwa.

Tambaya
Majalisar Dokoki ta Ƙasa ta kuma ƙirƙiro Hukumomin Raya Yankuna (Regional Development Commissions). Me ya sa aka ga akwai buƙatar hakan?

Kakakin Majalisa Abbas
An kafa Hukumomin Raya Yankunan ne domin hanzarta ci gaba a yankunan siyasar ƙasar nan.
Kowane yanki yana da nasa ƙalubalen ci gaba na musamman.
Waɗannan hukumomi za su ba da damar a mai da hankali kan abubuwan da suka fi muhimmanci ga kowane yanki, tare da ƙara ƙarfafa ƙoƙarin Gwamnatin Tarayya.
Mun yi imanin cewa za su taka muhimmiyar rawa wajen bunƙasa ci gaban ƙasa.

Tambaya
Batun tsaro ne ya mamaye tattaunawa a lokacin Makon Buɗaɗɗen Majalisar Dokoki ta Ƙasa (National Assembly Open Week). Mene ne manyan sakamakon da aka samu?

Kakakin Majalisa Abbas
Tsaro na ci gaba da kasancewa ɗaya daga cikin manyan ƙalubalen da Najeriya ke fuskanta.
Shi ya sa muka gayyaci shugabannin hukumomin tsaro, Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, Sarkin Zazzau, da tsohon Babban Hafsan Tsaron Ƙasa, Janar Lucky Irabor, tare da sauran masu ruwa da tsaki.
Bayan doguwar tattaunawa, mun fitar da sanarwar ƙarshe (communiqué) mai ɗauke da shawarwari kan yadda za a inganta tsarin tsaron Najeriya.
Mun kuma yi nazari kan ƙudirin dokar ‘Yan Sandan Jihohi (State Police Bill), sannan muka karɓi muhimman shawarwari daga mahalarta taron.

Tambaya
‘Yan Najeriya da dama suna nuna damuwa cewa gwamnonin jihohi na iya amfani da ‘Yan Sandan Jihohi wurin musgunawa Yan Adawa. Wani matakan kariya aka tanada?

Kakakin Majalisa Abbas
Mun yi la’akari da wannan damuwa sosai.
Ƙudirin dokar ya ƙunshi matakan daidaito da kariya (checks and balances) domin hana Amfani Dasu ta hanyar da bai dace ba.
Gwamnonin jihohi ba za su kasance da cikakken iko ba tare da iyaka kan tsarin gudanar da ‘yan sandan jihohi.
Haka kuma muna ƙarfafa ‘yan jarida da sauran masu ruwa da tsaki su yi nazarin ƙudirin dokar tare da gabatar da shawarwarinsu kafin a amince da ita a ƙarshe.

Tambaya
Majalisarku tana ba da shawarar ƙarin kujerun majalisa ga mata. Me ya sa kuka ɗauki wannan mataki?

Kakakin Majalisa Abbas
Yawan wakilcin mata a Najeriya har yanzu yana ƙasa da matakin da ya dace a tsarin dimokuraɗiyya.
Shawararmu ita ce a samar da kujerun da aka keɓe wa mata ta hanyar tsarin Kwalejin Zaɓe (Electoral College), tare da ci gaba da riƙe mazabu 360 na Majalisar Wakilai da ake da su yanzu.
Kowace jiha za ta sami ƙarin kujera guda ɗaya da za a keɓe ta ga mata kaɗai.
Hakazalika, ana ba da shawarar ƙarin kujeru 12 na Majalisar Dattawa, inda za a raba kujeru biyu ga kowace shiyya ta siyasa (geopolitical zone) bisa tsarin juyawa.
An tsara waɗannan matakan ne a matsayin na wucin gadi na tsawon shekaru 16, har sai mata sun samu damar yin takara cikin adalci a ƙarƙashin tsarin zaɓen da ake da shi.

Tambaya
Ana ganin kana da kyakkyawar alaƙar aiki da abokan aikinka Yan majalisar ba tare da saɓani ko rikici ba. Mene ne sirrin hakan?

Kakakin Majalisa Abbas
(Dariya…) Ina ganin ya kamata a yi wannan tambayar ga abokan aikina. Su ne suka fi dacewa su ba da amsa.
Sai dai, duk wani matsayin shugabanci da ka tsinci kanka a ciki, ka tabbatar da riƙon amana, gaskiya, adalci, daidaito da kuma tabbatar da adalci ga kowa.
Idan ka iya yin hakan, to za a sami zaman lafiya.
Wannan shi ne ainihin abin da muke yi a matsayin shugabannin Majalisar Wakilai.
Muna tabbatar da cewa ra’ayin kowa yana da muhimmanci, domin muna wakiltar Najeriya ne.

Tambaya
Wasu ‘yan Najeriya suna bayyana Majalisa zango ta 10 a matsayin Yan amshin shatan Shugaban Kasa Bola Tinubu. Ta yaya za ku mayar da martani kan hakan?

Kakakin Majalisa Abbas
Ban yarda da wannan ra’ayi kwata-kwata ba.
Majalisar Dokoki ta Ƙasa tana goyon bayan manufofin da muka yi imanin za su amfani ‘yan Najeriya.
Idan bangaren zartarwa ya gabatar da gyare-gyaren da suka yi daidai da ci gaban ƙasa, nauyin da kundin tsarin mulki ya ɗora mana shi ne mu yi nazarinsu sosai kafin mu amince da su.
Haɗin gwiwa mai ma’ana tsakanin bangaren zartarwa da na majalisa bai kamata a ɗauke shi a matsayin rauni ba.
A faɗin duniya, dimokuraɗiyyun da suka yi nasara suna aiki ne ta hanyar haɗin gwiwa tsakanin waɗannan bangarori biyu na gwamnati.
Nauyinmu shi ne yi wa ‘yan Najeriya hidima, ba wai mu riƙa adawa da manufofin gwamnati saboda dalilan siyasa kawai ba.
Ma’aunin gaskiya shi ne ko dokokin da aka samar suna amfanar da jama’a.
Na shafe shekaru goma sha shida (16) ina Majalisar Dokoki ta Ƙasa.
Ba mu taɓa samun ƙarin kuɗaɗen ayyukan mazabu ba sai a Majalisa zango ta 9, lokacin da aka ƙara Naira miliyan ɗari (₦100,000,000).
Amma a wannan zangon mulki, wato Majalisa ta 10, Mai Girma Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da ƙara wannan kuɗi zuwa Naira biliyan ɗaya (₦1,000,000,000) ga kowace mazaba domin amfanin ‘yan Najeriya.
Shin wannan ba shi ne ainihin ma’anar kyakkyawan shugabanci ba?
Mu a matsayin ‘yan majalisu bai kamata mu riƙa gaba da bangaren zartarwa ba, musamman idan bangarorin biyu suna ƙarƙashin jam’iyya ɗaya ta siyasa.
Abin da ake buƙata shi ne yanayin zaman lafiya da haɗin kai tsakanin bangaren zartarwa da na majalisa domin ci gaban ƙasa.

Kakakin Majalisar, Rt. Hon. Tajudeen Abbas, ya sake jaddada cewa Majalisar Dokoki ta Ƙasa ta 10 na ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da gaskiya da riƙon amana, shugabanci mai haɗa kowa da kowa, da kuma aiwatar da gyare-gyaren da za su ƙarfafa cibiyoyin dimokuraɗiyyar Najeriya.

Previous Post

NEMA ta kammala rabon kwandunan abinci 24,302 na KSrelief ga gidaje masu rauni a jihohi biyar

Next Post

Kamfanin NNPC Ta Yi Rijistar Riba N535bn Bayan Haraji a Yuni Shekara ta 2026

Related Posts

YANKIN AREWA TA ZABI HANYAR DA TAKESO: ABBAS NA JAMIYAR ADP YA GINA TSARI A KAN KANANAN HUKUMOMI 774 KAFIN 2027
Siyasa

YANKIN AREWA TA ZABI HANYAR DA TAKESO: ABBAS NA JAMIYAR ADP YA GINA TSARI A KAN KANANAN HUKUMOMI 774 KAFIN 2027

August 11, 2026
Shugabar Jamiyar LP ta yi kira da a yi zaɓen 2027 cikin lumana
Siyasa

Shugabar Jamiyar LP ta yi kira da a yi zaɓen 2027 cikin lumana

August 1, 2026
Gwamna Yusuf Ya Yi Kira Ga Matasa Lauyoyi Su Rungumi Gaskiya da Adalci
Siyasa

Gwamna Yusuf Ya Sake Jaddada Kudirinsa Na Aiwatar da Tsarin Cigaban Kano

July 16, 2026
Gwamna Yusuf Ya Kai Ziyaran Gaisuwa da Girmamawa ga Mataimakin Shugaban Kasa Shettima, Ya Taya Shi Murna Bisa Fitowarsa a Matsayin Abokin Takaran Tinubu
Siyasa

Gwamna Yusuf Ya Kai Ziyaran Gaisuwa da Girmamawa ga Mataimakin Shugaban Kasa Shettima, Ya Taya Shi Murna Bisa Fitowarsa a Matsayin Abokin Takaran Tinubu

July 13, 2026
Kotun Daukaka Kara Ta Tabbatar Da Shugabancin LP Na Nenadi Usman
Siyasa

Kotun Daukaka Kara Ta Tabbatar Da Shugabancin LP Na Nenadi Usman

July 7, 2026
Jigon ADC Kamaludeen Skeedo Ya ce Babu Batun Siyasar Jam’iyya a 2027, Ya Bukaci Gwamnatin Uba Sani Da Ta Gyara Kurakurenta
Siyasa

Jigon ADC Kamaludeen Skeedo Ya ce Babu Batun Siyasar Jam’iyya a 2027, Ya Bukaci Gwamnatin Uba Sani Da Ta Gyara Kurakurenta

July 4, 2026
Next Post
Shekarar Farko ta Bashir Bayo Ojulari a NNPC: Jagoranci, Manufa da Sabuwar Tsarin Makamashi

Kamfanin NNPC Ta Yi Rijistar Riba N535bn Bayan Haraji a Yuni Shekara ta 2026

Shugabar Jamiyar LP ta yi kira da a yi zaɓen 2027 cikin lumana

Shugabar Jamiyar LP ta yi kira da a yi zaɓen 2027 cikin lumana

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Trending
  • Comments
  • Latest
“Sayen Wayoyin Hannu Na Zuwa Da Mummunar Matsala” — Abubakar Ubale

“Sayen Wayoyin Hannu Na Zuwa Da Mummunar Matsala” — Abubakar Ubale

January 18, 2026
TARON OPEN MIC WITH SHINE YAFARA YUNKURIN FARFAƊO DA ƊABI’U: MASU JAWABI SUN YABI HANGEN NESAN MR. SHINE

TARON OPEN MIC WITH SHINE YAFARA YUNKURIN FARFAƊO DA ƊABI’U: MASU JAWABI SUN YABI HANGEN NESAN MR. SHINE

June 20, 2026
BA Zamu Sake Yarda ayi Watsi da Matasa Bayan Zabe ba Inji Kungiyar NYA

BA Zamu Sake Yarda ayi Watsi da Matasa Bayan Zabe ba Inji Kungiyar NYA

January 28, 2026
ADC ta samu babban jigo na siyasa Farfesa Sani Bello don aikin duba kundin tsarin mulki bayan Awanni 24 da barin APC

ADC Ta Nuna Sabuwar Zamanin Gaskiya da Aminci ta Hanyar Nada Farfesa Mohammed Sani Bell

January 8, 2026
Sanata Anthony Yaro Ya Gamsu Da Dokar Cin Zarafin yara

Sanata Anthony Yaro Ya Gamsu Da Dokar Cin Zarafin yara

0
Zamu Fara Bincike A Kan Matuka Jiragen Sama Don Hanasu Shan Kayan Maye, Inji Sanata Buhari Abdulfatah

Zamu Fara Bincike A Kan Matuka Jiragen Sama Don Hanasu Shan Kayan Maye, Inji Sanata Buhari Abdulfatah

0
Kudirin Dokar Cibiyar Hukumar EFCC Ta Tsallake karatu Na Biyu

Kudirin Dokar Cibiyar Hukumar EFCC Ta Tsallake karatu Na Biyu

0
Yan Majalisa da Ma’aikatar Yan Sanda sun goyi bayan kashi 15% na Mata Wurin daukar aiki

Yan Majalisa da Ma’aikatar Yan Sanda sun goyi bayan kashi 15% na Mata Wurin daukar aiki

0
Mauludi: Sabunta Alkawarinmu ga Zaman Lafiya, Tausayi da Jinƙai

Mauludi: Sabunta Alkawarinmu ga Zaman Lafiya, Tausayi da Jinƙai

August 26, 2026
Mauludi: Ku yi addu’ar farfaɗowar tattalin arziki da inganta tsaro — Ashiru ya roƙi al’ummar Musulmi

Mauludi: Ku yi addu’ar farfaɗowar tattalin arziki da inganta tsaro — Ashiru ya roƙi al’ummar Musulmi

August 25, 2026
Aikin Bonga Kudu-Maso-Yamma Aparo: NNPC, Ƙungiyoyin Maƙasanta na OML 118 Sun Kulla Ƙarin Yarjejeniyar PSC da DSA

Aikin Bonga Kudu-Maso-Yamma Aparo: NNPC, Ƙungiyoyin Maƙasanta na OML 118 Sun Kulla Ƙarin Yarjejeniyar PSC da DSA

August 24, 2026
Kamfanin Dangote Cement ta yi bikin Ranar Matasa a Obajana tare da sabunta kudirin ci gaban matasa.

Kamfanin Dangote Cement ta yi bikin Ranar Matasa a Obajana tare da sabunta kudirin ci gaban matasa.

August 19, 2026

Recent News

Mauludi: Sabunta Alkawarinmu ga Zaman Lafiya, Tausayi da Jinƙai

Mauludi: Sabunta Alkawarinmu ga Zaman Lafiya, Tausayi da Jinƙai

August 26, 2026
Mauludi: Ku yi addu’ar farfaɗowar tattalin arziki da inganta tsaro — Ashiru ya roƙi al’ummar Musulmi

Mauludi: Ku yi addu’ar farfaɗowar tattalin arziki da inganta tsaro — Ashiru ya roƙi al’ummar Musulmi

August 25, 2026
Aikin Bonga Kudu-Maso-Yamma Aparo: NNPC, Ƙungiyoyin Maƙasanta na OML 118 Sun Kulla Ƙarin Yarjejeniyar PSC da DSA

Aikin Bonga Kudu-Maso-Yamma Aparo: NNPC, Ƙungiyoyin Maƙasanta na OML 118 Sun Kulla Ƙarin Yarjejeniyar PSC da DSA

August 24, 2026
Kamfanin Dangote Cement ta yi bikin Ranar Matasa a Obajana tare da sabunta kudirin ci gaban matasa.

Kamfanin Dangote Cement ta yi bikin Ranar Matasa a Obajana tare da sabunta kudirin ci gaban matasa.

August 19, 2026
Kasuwancin Duniya

© 2025 Kasuwancin Duniya - Wanda ya tsara AuspiceWeb.

Kewaya Site

  • Gida
  • Game da Mu
  • Tuntuɓar
  • Advertise
  • Privacy & Policy

Biyo Mu

No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Kasuwanci
    • Noma
    • Mai da Iskar Gas
  • Al’adu da Fasaha
    • Kirkire-kirkire
    • Tafiye-tafiye
  • Fashin Baki
  • Hotuna masu ban Sha’awa
  • Ƙasashen Duniya
  • Wasanni

© 2025 Kasuwancin Duniya - Wanda ya tsara AuspiceWeb.

Powered by
►
Necessary cookies enable essential site features like secure log-ins and consent preference adjustments. They do not store personal data.
None
►
Functional cookies support features like content sharing on social media, collecting feedback, and enabling third-party tools.
None
►
Analytical cookies track visitor interactions, providing insights on metrics like visitor count, bounce rate, and traffic sources.
None
►
Advertisement cookies deliver personalized ads based on your previous visits and analyze the effectiveness of ad campaigns.
None
►
Unclassified cookies are cookies that we are in the process of classifying, together with the providers of individual cookies.
None
Powered by