Daga Bashir Bello, Abuja
Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sake jaddada kudirin gwamnatinsa na aiwatar da cikakken tsarin cigaba da aka tsara domin hanzarta sauyin tattalin arziki da zamantakewar al’umma a Kano.
Wannan na cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Laraba.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin taron da ya yi da shugabannin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) na kungiyoyin rumfunan zabe daga kananan hukumomi 44 na jihar.Gwamna Yusuf ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da mai da hankali wajen samar da nagartaccen mulki da inganta rayuwar jama’a.
Ya ce gwamnatinsa ba za ta bari siyasar batanci ta karkatar da ita ba, sai dai za ta ci gaba da aiwatar da ayyuka da shirye-shirye da za su bunkasa tattalin arziki, inganta ababen more rayuwa da kuma kyautata ayyukan gwamnati.
Gwamnan ya bayyana kwarin gwiwa cewa nasarorin gwamnatinsa za su ci gaba da samun amincewa da goyon bayan jama’a kafin babban zaben 2027.
Ya bayyana sabbin shugabannin jam’iyya da aka rantsar a matsayin cibiyar karfi ta tsarin jam’iyyar APC a matakin kasa.
Gwamna Yusuf ya bukace su da su kasance masu hadin kai da jajircewa wajen wayar da kan jama’a domin samun goyon bayan jam’iyya a rumfunan zabe, mazabu da kananan hukumomin su.
Ya tabbatar musu da ci gaba da samun tallafi ta hanyar shirye-shiryen karfafa gwiwa da gina kwarewa domin karfafa jam’iyya a matakin kasa.
Gwamna Yusuf ya bayyana fata cewa APC za ta samu nasarori masu rinjaye a babban zaben 2027 ta hanyar hadin kai, jajircewa da ci gaba da tuntubar jama’a.





















